< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
Salmo di Davide, [dato] al Capo de' Musici; intorno a ciò che il profeta Natan venne a lui, dopo ch'egli fu entrato da Bet-seba ABBI pietà di me, o Dio, secondo la tua benignità; Secondo la moltitudine delle tue compassioni, cancella i miei misfatti.
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Lavami molto e molto della mia iniquità, E nettami del mio peccato.
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
Perciocchè io conosco i miei misfatti, E il mio peccato [è] del continuo davanti a me.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
Io ho peccato contro a te solo, Ed ho fatto quello che ti dispiace; [Io lo confesso], acciocchè tu sii riconosciuto giusto nelle tue parole, [E] puro ne' tuoi guidicii.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
Ecco, io sono stato formato in iniquità; E la madre mia mi ha conceputo in peccato.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
Ecco, ti è piaciuto insegnarmi verità nell'interiore, E sapienza nel di dentro.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Purgami con isopo, e sarò netto; Lavami, e sarò più bianco che neve.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Fammi udire gioia ed allegrezza; [Fa' che] le ossa che tu hai tritate, festeggino.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Nascondi la tua faccia da' miei peccati, E cancella tutte le mie iniquità.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
O Dio, crea in me un cuor puro, E rinnovella dentro di me uno spirito diritto.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
Non rigettarmi dalla tua faccia; E non togliermi lo Spirito tuo santo.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Rendimi l'allegrezza della tua salute; E [fa' che] lo Spirito volontario mi sostenga.
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
Io insegnerò le tue vie a' trasgressori; E i peccatori si convertiranno a te.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Liberami dal sangue, o Dio, Dio della mia salute; La mia lingua canterà con giubilo la tua giustizia.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
Signore, aprimi le labbra; E la mia bocca racconterà la tua lode.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
Perciocchè tu non prendi piacere in sacrificio; Altrimenti io l'avrei offerto; Tu non gradisci olocausto.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
I sacrificii di Dio [sono] lo spirito rotto; O Dio, tu non isprezzi il cuor rotto e contrito.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Fa' del bene a Sion per la tua benevolenza; Edifica le mura di Gerusalemme.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Allora prenderai piacere in sacrificii di giustizia, In olocausti, e in offerte da ardere interamente; Allora si offeriranno giovenchi sul tuo Altare.

< Zabura 51 >