< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
For the chief musician. A psalm of David; when Nathan the prophet came to him after he had slept with Bathsheba. Have mercy on me, God, because of your covenant faithfulness; for the sake of the multitude of your merciful actions, blot out my transgressions.
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Wash me thoroughly from my iniquity and cleanse me from my sin.
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
For I know my transgressions, and my sin is always before me.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
Against you, you only, I have sinned and done what is evil in your sight; you are right when you speak; you are correct when you judge.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
See, I was born in iniquity; as soon as my mother conceived me, I was in sin.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
See, you desire trustworthiness in my inner self; and you teach me wisdom in the secret place within.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Purify me with hyssop, and I will be clean; wash me, and I will be whiter than snow.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Make me hear joy and gladness so that the bones that you have broken may rejoice.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Hide your face from my sins and blot out all my iniquities.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
Create in me a clean heart, God, and renew a right spirit within me.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
Do not drive me away from your presence, and do not take your holy Spirit from me.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Restore to me the joy of your salvation, and sustain me with a willing spirit.
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
Then will I teach transgressors your ways, and sinners will be converted to you.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Forgive me for shedding blood, God of my salvation, and I will shout for the joy of your righteousness.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
Lord, open my lips, and my mouth will express your praise.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
For you do not delight in sacrifice, or I would give it; you have no pleasure in burnt offerings.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
The sacrifices of God are a broken spirit. You, God, will not despise a broken and a contrite heart.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Do good in your good pleasure to Zion; rebuild the walls of Jerusalem.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Then will you delight in the sacrifices of righteousness, in burnt offerings and whole burnt offerings; then our people will offer bulls on your altar.

< Zabura 51 >