< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
“To the chief musician, a psalm of David, When Nathan the prophet came unto him, after he had gone in unto Bath-sheba'.” Be gracious unto me, O God, according to thy kindness: according to the greatness of thy mercies blot out my transgressions.
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Wash me thoroughly from my iniquity, and cleanse me from my sin.
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
For of my transgressions I have full knowledge; and my sin is before me continually.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
To thee, thee only, have I sinned, and what is evil in thy eyes have I done: —in order that thou mightest be righteous when thou speakest, be justified when thou judgest.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
Behold, in iniquity was I brought forth; and in sin did my mother conceive me.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
Behold, thou desirest truth in the inward parts: therefore do thou cause me to know wisdom in the recesses [of the heart].
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Cleanse me from sin with hyssop, and I shall be clean: wash me, and I shall be whiter than snow.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Cause me to hear gladness and joy; that the bones which thou hast crushed may rejoice.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Hide thy face from my sins, and all my iniquities do thou blot out.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
Create unto me a clean heart, O God; and a firm spirit renew thou within me.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
Cast me not away from thy presence; and thy holy spirit do not take from me.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Restore unto me the gladness of thy salvation; and with a liberal spirit do thou support me.—
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
I will teach transgressors thy ways, and sinners shall return unto thee.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Deliver me from blood-guiltiness, O God, thou God of my salvation; [that] my tongue may sing aloud of thy righteousness.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
O Lord, open thou my lips, and my mouth shall declare thy praise.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
For thou desirest not sacrifice; else would I give it: in burnt-offering hast thou no delight.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
The sacrifices of God are a broken spirit: a broken and a contrite heart, O God, wilt thou not despise.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Do good in thy favor unto Zion; build thou the walls of Jerusalem.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Then wilt thou be pleased with the sacrifices of righteousness, with burnt-offering and entire offering: then shall bullocks be offered upon thy altar.

< Zabura 51 >