< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
Have mercy on me, O God, according to your loving kindness: according to the multitude of your tender mercies blot out my transgressions.
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Wash me thoroughly from my iniquity, and cleanse me from my sin.
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
For I acknowledge my transgressions: and my sin is ever before me.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
Against you, you only, have I sinned, and done this evil in your sight: that you might be justified when you speak, and be clear when you judge.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
Behold, I was shaped in iniquity; and in sin did my mother conceive me.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
Behold, you desire truth in the inward parts: and in the hidden part you shall make me to know wisdom.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Purge me with hyssop, and I shall be clean: wash me, and I shall be whiter than snow.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Make me to hear joy and gladness; that the bones which you have broken may rejoice.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Hide your face from my sins, and blot out all my iniquities.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
Create in me a clean heart, O God; and renew a right spirit within me.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
Cast me not away from your presence; and take not your holy spirit from me.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Restore to me the joy of your salvation; and uphold me with your free spirit.
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
Then will I teach transgressors your ways; and sinners shall be converted to you.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Deliver me from bloodguiltiness, O God, you God of my salvation: and my tongue shall sing aloud of your righteousness.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
O Lord, open you my lips; and my mouth shall show forth your praise.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
For you desire not sacrifice; else would I give it: you delight not in burnt offering.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
The sacrifices of God are a broken spirit: a broken and a contrite heart, O God, you will not despise.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Do good in your good pleasure to Zion: build you the walls of Jerusalem.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Then shall you be pleased with the sacrifices of righteousness, with burnt offering and whole burnt offering: then shall they offer bullocks on your altar.

< Zabura 51 >