< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
For the end, a Psalm of David, when Nathan the prophet came to him, when he had gone to Bersabee. Have mercy upon me, O God, according to thy great mercy; and according to the multitude of thy compassions blot out my transgression.
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Wash me thoroughly from mine iniquity, and cleanse me from my sin.
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
For I am conscious of mine iniquity; and my sin is continually before me.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
Against thee only have I sinned, and done evil before thee: that thou mightest be justified in thy sayings, and mightest overcome when thou art judged.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
For, behold, I was conceived in iniquities, and in sins did my mother conceive me.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
For, behold, thou lovest truth: thou hast manifested to me the secret and hidden things of thy wisdom.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Thou shalt sprinkle me with hyssop, and I shall be purified: thou shalt wash me, and I shall be made whiter than snow.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Thou shalt cause me to hear gladness and joy: the afflicted bones shall rejoice.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Turn away thy face from my sins, and blot out all mine iniquities.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
Create in me a clean heart, O God; and renew a right spirit in my inward parts.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
Cast me not away from thy presence; and remove not thy holy Spirit from me.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Restore to me the joy of thy salvation: establish me with thy directing Spirit.
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
[Then] will I teach transgressors thy ways; and ungodly men shall turn to thee.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Deliver me from blood-guiltiness, O God, the God of my salvation: [and] my tongue shall joyfully declare thy righteousness.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
O Lord, thou shalt open my lips; and my mouth shall declare thy praise.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
For if thou desiredst sacrifice, I would have given [it]: thou wilt not take pleasure in whole-burnt-offerings.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
Sacrifice to God is a broken spirit: a broken and humbled heart God will not despise.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Do good, O Lord, to Sion in thy good pleasure; and let the walls of Jerusalem be built.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Then shalt thou be pleased with a sacrifice of righteousness, offering, and whole-burnt-sacrifices: then shall they offer calves upon thine altar.

< Zabura 51 >