< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
(Til sangmesteren. En salme af David, dengang Natan kom til ham, efter at han havde været inde hos Batseba.) Gud, vær mig nådig efter din Miskundhed, udslet mine Overtrædelser efter din store Barmhjertighed,
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
tvæt mig fuldkommen ren for min Skyld og rens mig for min Synd!
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
Mine Overtrædelser kender jeg jo, min Synd står mig altid for Øje.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
Mod dig har jeg syndet, mod dig alene, og gjort, hvad i dine Øjne er ondt, at du må få Ret, når du taler, stå ren, når du dømmer.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
Se, jeg er født i Misgerning, min Moder undfanged mig i Synd.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
Du elsker jo Sandhed i Hjertets Løndom, så lær mig da Visdom i Hjertedybet.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Rens mig for Synd med Ysop, tvæt mig hvidere end Sne;
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
mæt mig med Fryd og Glæde, lad de Ben, du knuste, juble;
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
skjul dit Åsyn for mine Synder, udslet alle mine Misgerninger;
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
skab mig, o Gud, et rent Hjerte, giv en ny, en stadig Ånd i mit Indre;
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
kast mig ikke bort fra dit Åsyn, tag ikke din hellige Ånd fra mig;
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
glæd mig igen med din Frelse, giv mig til Støtte en villig Ånd!
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
Da vil jeg lære Overtrædere dine Veje, og Syndere skal vende om til dig.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Fri mig fra Blodskyld, Gud, min Frelses Gud, så skal min Tunge lovsynge din Retfærd;
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
Herre, åben mine Læber, så skal min Mund forkynde din Pris.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
Thi i Slagtoffer har du ikke Behag, og gav jeg et Brændoffer, vandt det dig ikke.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
Offer for Gud er en sønderbrudt Ånd; et sønderbrudt, sønderknust Hjerte agter du ikke ringe, o Gud.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Gør vel i din Nåde mod Zion, opbyg Jerusalems Mure!
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Da skal du have Behag i rette Ofre, Brænd- og Heloffer, da bringes Tyre op på dit Alter.

< Zabura 51 >