< Zabura 50 >

1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
En psalm av Asaf. Gud, HERREN Gud, talar och kallar jorden, allt mellan öster och väster.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Från Sion, skönhetens fullhet, träder Gud fram i glans.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Vår Gud kommer, och han skall icke tiga. Förtärande eld går framför honom, och omkring honom stormar det med makt.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
Han kallar på himmelen därovan och på jorden, för att döma sitt folk:
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
"Församlen till mig mina fromma, som sluta förbund med mig vid offer."
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Och himlarna förkunna att han är rättfärdig, att Gud är den som skipar rätt. (Sela)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Hör, mitt folk, jag vill tala; Israel, låt mig varna dig. Gud, din Gud, är jag.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Icke för dina slaktoffer vill jag gå till rätta med dig; dina brännoffer har jag alltid inför mig.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
Jag vill icke taga tjurar ur ditt hus eller bockar ur dina fållor;
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
ty mina äro alla skogens djur, boskapen på de tusende bergen;
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
jag känner alla fåglar på bergen, och vad som rör sig på marken är mig bekant.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
Om jag hungrade, skulle jag icke säga dig det; ty min är jordens krets med allt vad därpå är.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Skulle jag äta tjurars kött, och skulle jag dricka bockars blod?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Nej, offra lovets offer åt Gud, så skall du få infria dina löften till den Högste.
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
Och åkalla mig i nöden, så vill jag hjälpa dig, och du skall prisa mig."
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Men till den ogudaktige säger Gud: "Huru kan du tala om mina stadgar och föra mitt förbund på tungan,
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
du som hatar tuktan och kastar mina ord bakom dig?
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
Om du ser en tjuv, så håller du med honom, och med äktenskapsbrytare giver du dig i lag.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Din mun släpper du lös till vad ont är, och din tunga hopspinner svek.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Du sitter där och förtalar din broder, din moders son lastar du!
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
Så gör du, och jag tiger, och nu tror du att jag är såsom du. Nej, jag vill straffa dig och ställa dig det för ögonen.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
I som förgäten Gud, märken detta, för att jag icke må sönderriva eder utan räddning:
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
den som offrar lovets offer, han ärar mig; och den som aktar på sin väg, honom skall jag låta se Guds frälsning."

< Zabura 50 >