< Zabura 50 >
1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
En Psalm Assaphs. Herren Gud den mägtige talar, och kallar verldena, ifrå solenes uppgång, allt intill nedergången.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Af Zion går upp Guds härliga sken.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Vår Gud kommer, och tiger intet. Förtärande eld går för honom, och omkring honom en mägtig storm.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
Han kallar himmel och jord, att han skall döma sitt folk.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
Församler mig mina heliga, som förbundet mer akta än offer.
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Och himlarna skola förkunna hans rättfärdighet; ty Gud är domaren. (Sela)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Hör, mitt folk, låt mig tala; Israel, låt mig ibland dig betyga: Jag Gud är din Gud.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
För ditt offers skull straffar jag dig intet; äro dock dine bränneoffer alltid för mig.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
Jag vill icke taga oxar utu ditt hus, eller bockar utu dine stall;
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
Ty all djur i skogenom äro mine, och boskapen på bergen, der de vid tusendetal gå.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
Jag känner alla foglar på bergen, och allahanda djur på markene äro för mig.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
Om mig hungrade, ville jag intet säga dig deraf; ty jordenes krets är min, och allt det deruti är.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Menar du, att jag oxakött äta vill, eller bockablod dricka?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Offra Gudi tackoffer, och betala dem Högsta ditt löfte.
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
Och åkalla mig i nödene; så vill jag hjelpa dig, så skall du prisa mig.
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Men till den ogudaktige säger Gud: Hvi förkunnar du mina rätter, och tager mitt förbund i din mun;
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Efter du dock hatar tuktan, och kastar min ord bakom dig?
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
När du ser en tjuf, så löper du med honom, och hafver din del med horkarlar.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Din mun låter du tala det ondt är, och din tunga bedrifver falskhet.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Du sitter och talar emot din broder; dine moders son förtalar du.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
Detta gör du, och jag tiger. Det menar du, att jag skulle vara lika som du; men jag skall straffa dig, och sätta dig det under ögonen.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Märker dock det, I som Gud förgäten, att jag icke en gång bortrycker, och är så ingen förlösare mer.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Den der tack offrar, han prisar mig; och der är vägen, att jag visar honom Guds salighet.