< Zabura 50 >

1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
Zaburi ya Asafu. Mwenye Nguvu, Mungu, Bwana, asema na kuiita dunia, tangu mawio ya jua hadi mahali pake liendapo kutua.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Kutoka Sayuni, penye uzuri mkamilifu, Mungu anaangaza.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Mungu wetu anakuja na hatakaa kimya, moto uteketezao unamtangulia, akiwa amezungukwa na tufani kali.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
Anaziita mbingu zilizo juu, na nchi, ili aweze kuwahukumu watu wake:
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
“Nikusanyieni watu wangu waliowekwa wakfu, waliofanya agano nami kwa dhabihu.”
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Nazo mbingu zinatangaza haki yake, kwa maana Mungu mwenyewe ni hakimu.
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
“Sikieni, enyi watu wangu, nami nitasema, ee Israeli, nami nitashuhudia dhidi yenu: Mimi ndimi Mungu, Mungu wenu.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Sikukemei kwa sababu ya dhabihu zako, au sadaka zako za kuteketezwa, ambazo daima ziko mbele zangu.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
Sina haja ya fahali wa banda lako, au mbuzi wa zizi lako.
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
Kwa maana kila mnyama wa msituni ni wangu, na pia makundi ya mifugo juu ya vilima elfu.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
Ninamjua kila ndege mlimani, nao viumbe wa kondeni ni wangu.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
Kama ningekuwa na njaa, nisingewaambia ninyi, kwa maana ulimwengu ni wangu, pamoja na vyote vilivyomo ndani yake.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Je, mimi hula nyama ya mafahali au kunywa damu ya mbuzi?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Toa sadaka za shukrani kwa Mungu, timiza nadhiri zako kwake Yeye Aliye Juu Sana,
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
na uniite siku ya taabu; nami nitakuokoa, nawe utanitukuza.”
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Lakini kwake mtu mwovu, Mungu asema: “Una haki gani kunena sheria zangu au kuchukua agano langu midomoni mwako?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Unachukia mafundisho yangu na kuyatupa maneno yangu nyuma yako.
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
Unapomwona mwizi, unaungana naye, unapiga kura yako pamoja na wazinzi.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Unakitumia kinywa chako kwa mabaya na kuuongoza ulimi wako kwa hila.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Wanena daima dhidi ya ndugu yako na kumsingizia mwana wa mama yako.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
Mambo haya unayafanya, nami nimekaa kimya, ukafikiri Mimi nami ni kama wewe. Lakini nitakukemea na kuweka mashtaka mbele yako.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
“Yatafakarini haya, ninyi mnaomsahau Mungu, ama sivyo nitawararua vipande vipande, wala hapatakuwepo na yeyote wa kuwaokoa:
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Atoaye dhabihu za shukrani ananiheshimu mimi, naye aiandaa njia yake ili nimwonyeshe wokovu wa Mungu.”

< Zabura 50 >