< Zabura 50 >

1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
Un Salmo de Asaf. ¡El Señor, el Dios todopoderoso, habla! Él convoca a todos en la tierra, desde el este hasta el oeste.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Dios brilla desde el monte de Sión, perfecto en belleza.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Nuestro Dios llegará, y no se quedará quieto. Llamas de fuego vienen detrás de él, quemando todo a su alrededor; una feroz tormenta se mueve alrededor de él.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
Invoca a los cielos sobre la tierra para que presencien el juicio de su pueblo.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
“Tráiganme a los que confían en mí, aquellos que cumplieron mi pacto conmigo como sacrificio”.
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Los cielos declaran que sus decisiones están bien, porque Dios mismo es el juez. (Selah)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
“Mi pueblo, escuchen lo que tengo para decir. Traigo cargos en su contra, Israel. ¡Yo soy Dios, su Dios!
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
No estoy hablando de sacrificios ni de ofrendas quemadas que me ofrecen todo el tiempo.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
No necesito toros de sus graneros ni cabras de sus corrales,
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
porque míos son todos los animales del bosque, y el ganado de miles de cerros me pertenece.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
Conozco a cada pájaro de la montaña; todas las cosas vivientes en los campos son mías.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
Si estuviera hambriento, no te lo diría, porque la tierra y todo lo que hay en ella es mío.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
¿Me como yo la carne de los toros y bebo la sangre de las cabras?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Den ofrendas de agradecimiento a Dios; mantengan las promesas que le hicieron al Altísimo,
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
y llámenme cuando estén en problemas. Los rescataré, y me agradecerán”.
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Pero a los malvados Dios les dice, “¿Cuál es el objetivo de repetir mi ley y hacer promesas vacías sobre obedecer mi pacto?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Odias mi disciplina, y desechas mis palabras.
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
Cuando ves a la gente robando los admiras y te asocias con adúlteros.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Con tu boca dices cosas malas; usas tu lengua para esparcir mentiras.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Te sientas y comienzas a hablar en contra de tu hermano, calumniando al hijo de tu propia madre.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
Yo me quedo callado cuando haces esas cosas. Tú pensaste que yo era alguien como tú. Pero ahora te confronto, y traigo mis cargos en contra tuya.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Piensen otra vez, ustedes que menosprecian a Dios, o los haré trizas, y nadie podrá salvarlos.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Pero aquellos que dan ofrendas de agradecimiento me honran, y a aquellos que siguen el bien les mostraré mi salvación”.

< Zabura 50 >