< Zabura 50 >

1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
Mogočen Bog, celó Gospod, je spregovoril in poklical zemljo od sončnega vzhoda do njegovega zahoda.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
S Siona, popolne lepote, je zasijal Bog.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Naš Bog bo prišel in ne bo molčal. Ogenj bo požiral pred njim in okoli njega bo zelo viharno.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
Klical bo k nebesom od zgoraj in k zemlji, da bo lahko sodil svoje ljudstvo.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
»Zberite k meni moje svete, tiste, ki so z žrtvijo sklenili zavezo z menoj.«
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Nebesa bodo oznanjala njegovo pravičnost, kajti sam Bog je sodnik. (Sela)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
»Poslušaj, oh moje ljudstvo in govoril bom, oh Izrael in pričeval bom zoper tebe. Jaz sem Bog, celó tvoj Bog.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Ne bom te grajal zaradi tvojih klavnih daritev ali tvojih žgalnih daritev, da so bile nenehno pred menoj.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
Iz tvoje hiše ne bom vzel nobenega bikca niti kozlov iz tvojih staj.
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
Kajti vsaka gozdna žival je moja in živina na tisočêrih hribih.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
Poznam vso gorsko perjad in divje poljske živali so moje.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
Če bi bil lačen, ti ne bi povedal, kajti zemeljski [krog] je moj in njegova polnost.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Mar bom jedel meso bikov ali pil kri koz?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Bogu daruj zahvaljevanje in svoje zaobljube izpolni Najvišjemu.
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
Obrni se k meni v dnevu stiske, osvobodil te bom in ti me boš proslavil.«
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Toda zlobnemu Bog govori: »Kaj delaš, da oznanjaš moje zakone ali da v svoja usta jemlješ mojo zavezo?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Ker sovražiš poučevanje in moje besede zavračaš za seboj.
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
Ko vidiš tatu, se strinjaš z njim in si postal soudeleženec z zakonolomci.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Svoja usta izročaš v zlo in tvoj jezik snuje prevaro.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Sediš in govoriš zoper svojega brata, obrekuješ sina svoje matere.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
Te stvari si storil, jaz pa sem molčal. Mislil si, da sem bil povsem takšen kakor ti. Toda grajal te bom in jih v vrsti postavil pred tvoje oči.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Torej preudarite to, vi, ki pozabljate Boga, da vas ne bom raztrgal na koščke in nikogar ne bo, da osvobodi.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Kdorkoli daruje hvalo, me poveličuje in tistemu, ki pravilno ureja svoje vedênje, bom pokazal Božjo rešitev duše.«

< Zabura 50 >