< Zabura 50 >
1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
Salmo de Asafe: Deus, o SENHOR Deus fala e chama a terra, desde onde o sol nasce até onde ele se põe.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Desde Sião, a perfeição da beleza, Deus mostra seu imenso brilho.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Nosso Deus virá, e não ficará calado; fogo queimará adiante dele, e ao redor dele haverá grande tormenta.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
Ele chamará aos céus do alto, e à terra, para julgar a seu povo.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
Ajuntai-me meus santos, que confirmam meu pacto por meio de sacrifício.
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
E os céus anunciarão sua justiça, pois o próprio Deus é o juiz. (Selá)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Ouve, povo meu, e eu falarei; eu darei testemunho contra ti, Israel; eu sou Deus, o teu Deus.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Eu não te repreenderei por causa de teus sacrifícios, porque teus holocaustos estão continuamente perante mim.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
Não tomarei bezerro de tua casa, [nem] bodes de teus currais;
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
Porque todo animal das matas é meu, [e também] os milhares de animais selvagens das montanhas.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
Conheço todas as aves das montanhas, e as feras do campo [estão] comigo.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
Se eu tivesse fome, não te diria, porque meu é o mundo, e tudo o que nele há.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Comeria eu carne de touros, ou beberia sangue de bodes?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Oferece a Deus sacrifício de louvor, e paga ao Altíssimo os teus votos.
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
E clama a mim no dia da angústia; e eu te farei livre, e tu me glorificarás.
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Mas Deus diz ao perverso: Para que tu recitas meus estatutos, e pões meu pacto em tua boca?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Pois tu odeias a repreensão, e lança minhas palavras para detrás de ti.
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
Se vês ao ladrão, tu consentes com ele; e tens tua parte com os adúlteros.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Com tua boca pronuncias o mal, e tua língua gera falsidades.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Tu te sentas [e] falas contra teu irmão; contra o filho de tua mãe tu dizes ofensas.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
Tu fazes estas coisas, e eu fico calado; pensavas que eu seria como tu? Eu te condenarei, e mostrarei [teus males] diante de teus olhos.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Entendei, pois, isto, vós que vos esqueceis de Deus; para que eu não [vos] faça em pedaços, e não haja quem [vos] livre.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Quem oferece sacrifício de louvor me glorificará, e ao que cuida de seu caminho, eu lhe mostrarei a salvação de Deus.