< Zabura 50 >
1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
psalmus Asaph Deus deorum Dominus locutus est et vocavit terram a solis ortu usque ad occasum
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
ex Sion species decoris eius
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Deus manifeste veniet Deus noster et non silebit ignis in conspectu eius exardescet et in circuitu eius tempestas valida
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
advocabit caelum desursum et terram discernere populum suum
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
congregate illi sanctos eius qui ordinant testamentum eius super sacrificia
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
et adnuntiabunt caeli iustitiam eius quoniam Deus iudex est diapsalma
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
audi populus meus et loquar tibi Israhel et testificabor tibi Deus Deus tuus ego sum
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
non in sacrificiis tuis arguam te holocausta autem tua in conspectu meo sunt semper
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
non accipiam de domo tua vitulos neque de gregibus tuis hircos
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
quoniam meae sunt omnes ferae silvarum iumenta in montibus et boves
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
cognovi omnia volatilia caeli et pulchritudo agri mecum est
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
si esuriero non dicam tibi meus est enim orbis terrae et plenitudo eius
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
numquid manducabo carnes taurorum aut sanguinem hircorum potabo
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
immola Deo sacrificium laudis et redde Altissimo vota tua
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
et invoca me in die tribulationis et eruam te et honorificabis me diapsalma
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
peccatori autem dixit Deus quare tu enarras iustitias meas et adsumis testamentum meum per os tuum
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
tu vero odisti disciplinam et proiecisti sermones meos retrorsum
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
si videbas furem currebas cum eo et cum adulteris portionem tuam ponebas
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
os tuum abundavit malitia et lingua tua concinnabat dolos
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
sedens adversus fratrem tuum loquebaris et adversus filium matris tuae ponebas scandalum
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
haec fecisti et tacui existimasti inique quod ero tui similis arguam te et statuam contra faciem tuam
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
intellegite nunc haec qui obliviscimini Deum nequando rapiat et non sit qui eripiat
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
sacrificium laudis honorificabit me et illic iter quod ostendam illi salutare Dei