< Zabura 50 >

1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
[Psalm lal Asaph] LEUM GOD, God Kulana, El kaskas; El pangon faclu nufon, mutawauk kutulap na nwe roto.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Kalem lun God saromrom Zion me, Siti se su oaskulana in woiya.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
God lasr El tuku, tuh El tia tuku misla; Sie e lulap fah fahsr meet lukel, Ac sie eng upa raunella.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
El pangon kusrao ac faclu elos in orek loh kac, Ac liye ke El ac nununku mwet lal.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
El fahk ouinge, “Eisani mwet oaru luk nu yuruk, Elos su tuh orek wulela yuruk ke mwe kisa.”
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Kusrao fahkak lah God El suwoswos, Ac El sifacna pa Mwet Nununku.
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
“Porongo, kowos mwet luk, ac nga ac fah kaskas; Nga fah kaskas lain kom, Israel. Tuh nga God, God lom.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Ke nga kai kom, tia ma ke sripen mwe kisa lom Ku ke mwe kisa firir su kom use nu sik pacl e nukewa.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
Tusruktu nga tia enenu cow mukul liki ima lom, Ku nani liki un kosro nutum.
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
Kosro nukewa insak uh ma nutik, Ac oayapa cow su muta fin tausin inging.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
Won lemnak nukewa ma nutik Ac ma moul nukewa in imae.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
“Nga fin masrinsral, nga ac tia siyuk sum ke mwe mongo, Mweyen faclu ac koano nufon ma luk.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Ya nga kang ikwen cow mukul uh, Ku nim srahn nani uh?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Nga God Fulatlana! Pa inge mwe kisa ma nga enenu sum: In sang kulo ke insiom, ac in akfalye ma kom wulela kac.
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
Pre nu sik ke pacl mwe ongoiya sikyak; Nga ac fah molikomla, Ac kom fah kaksakinyu.”
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
A God El fahk nu sin mwet koluk, “Efu ku kom in fahkak ma sap luk? Efu ku kom in sramsram ke wulela luk?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Kom tia lungse nga in aksuwosye kom; Kom pilesru ma sap luk.
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
Kom asruoki nu sin mwet pisrapasr nukewa kom liye, Ac kom insese yurin mukul ac mutan su tia karinganang wulela in marut la.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
“Pacl nukewa kom akola in kaskas koluk, Ac kom tia tupwek in kaskas kikiap.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Kom akola in akkolukye mwet lom sifacna, Ac suk mwatan mwet lim.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
Kom oru ma inge nukewa, ac nga tia fahk kutena ma, Pwanang kom nunku mu nga oana kom. Tusruktu inge nga kai kom kac Tuh in kalem sum.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
“Porongo ma inge, kowos su pilesreyu. Kowos fin tia, nga fah kunauskowosla, Na wangin sie ac fah molikowosla.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Sang kulo pa mwe kisa se ma akfulatyeyu, Ac nga fah molelosla nukewa su akosyu.”

< Zabura 50 >