< Zabura 50 >
1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
Ein Psalm Asafs. / El Elohim Jahwe: Er redet / Und ruft der Erde d vom Aufgang der Sonne bis zum Niedergang.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Aus Zion, der Schönheit Krone, / Strahlt Elohim hervor.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Unser Gott, er kommt und schweiget nicht. / Verzehrend Feuer geht vor ihm her, / Rings um ihn stürmt es gewaltig.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
Er ruft die Himmel droben herbei. / Und die Erde, sein Volk zu richten:
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
"Versammelt mir die Frommen, / Die den Bund mit mir im Opfer geschlossen!"
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Die Himmel künden seine Gerechtigkeit; / Denn Elohim — er ist's, der richtet! (Sela)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
"Höre, mein Volk, o laß mich reden! / Israel, laß mich dich warnen! / Elohim, dein Gott, bin ich.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Nicht deiner Schlachtopfer wegen rüge ich dich — / Sind doch deine Brandopfer immer vor mir.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
Nicht brauche ich Stiere aus deinem Hause / Noch Böcke aus deinen Hürden.
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
Denn mein ist alles Wild des Waldes, / Das viele Getier auf den Bergen.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
Ich kenne jeden Vogel der Berge, / Und was auf den Feldern sich regt, ist mein.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
Sollte mich hungern, dir sagte ich's nicht. / Denn mein ist der Erdkreis und was ihn erfüllt.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Esse ich etwa der Stiere Fleisch / Und trink ich der Böcke Blut?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Opfere Elohim Dank / Und bezahle dem Höchsten deine Gelübde!
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
"Rufe mich an am Tage der Not: / Dann will ich dich retten, daß du mich ehrest."
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Aber zum Frevler spricht Elohim: / Wie? du zählst meine Satzungen auf / Und redest von meinem Bund?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Das wagst du und hasset doch Zucht / Und wirfst meine Worte hinter dich?
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
Siehst du einen Dieb, so gesellst du dich ihm, / Und mit Ehebrechern gehest du um.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Du lässest deinen Mund zum Bösen los, / Und deine Zunge spinnet Trug.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Mit andern verleumdest du deinen Bruder, / Deiner Mutter Sohn hängst du Schande an.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
Das hast du getan, und ich schwieg dazu. / Da dachtest du denn: ich wäre wie du. / Aber ich will dich zur Rechenschaft ziehn, / Dir's unter die Augen stellen."
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Merkt das wohl, die ihr Gottes vergeßt; / Sonst werd ich zerreißen, und niemand rettet.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Wer Dank opfert, der ehret mich recht, / Und er bahnet den Weg, / Auf dem ich ihm zeige das Heil Elohims.