< Zabura 50 >

1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
Psaume d’Asaph.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
C’est de Sion que vient l’éclat de sa splendeur.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Dieu viendra manifestement: notre Dieu viendra, et il ne gardera pas le silence.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
D’en haut il appellera le ciel et la terre pour juger son peuple.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
Rassemblez-lui ses saints, qui exécutent son alliance sur les sacrifices.
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Et les cieux annonceront sa justice, parce que c’est Dieu lui-même qui est juge.
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Écoute, mon peuple, et je parlerai; Israël, écoute; car je te prendrai à témoin: Dieu, ton Dieu, c’est moi qui le suis.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Je ne te reprendrai pas pour tes sacrifices; car tes holocaustes sont toujours en ma présence.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
Je ne prendrai pas des veaux de ta maison, ni des boucs de tes troupeaux.
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
Parce qu’à moi sont toutes les bêtes des forêts, les animaux qui paissent sur les montagnes et les bœufs.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
Je connais tous les volatiles du ciel, et la beauté des champs est en mon pouvoir.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
Si j’ai faim, je ne te le dirai pas: car à moi est le globe de la terre, et sa plénitude.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Est-ce que je mangerai des chairs de taureaux? ou boirai-je du sang des boucs?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Immole à Dieu un sacrifice de louange, et rends au Très-Haut tes vœux.
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
Et invoque-moi, au jour de la tribulation: je te délivrerai, et tu m’honoreras.
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Mais au pécheur Dieu a dit: Pourquoi racontes-tu mes justices, et pourquoi ta bouche annonce-t-elle mon alliance?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Pour toi, tu hais la discipline, et tu as rejeté ma parole derrière toi.
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
Si tu voyais un voleur, tu courais avec lui, et c’est avec les adultères que tu mettais ta part.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Ta bouche a abondé en malice, et ta langue ajustait des fourberies.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Assis, tu parlais contre ton frère et contre le fils de ta mère, tu posais une pierre d’achoppement.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
Tu as fait ces choses, et je me suis tu.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Comprenez ces choses, vous qui oubliez Dieu; de peur qu’un jour il ne vous enlève, et qu’il n’y ait personne qui vous délivre.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
C’est un sacrifice de louange qui m’honorera; et c’est là le chemin par lequel je lui montrerai le salut de Dieu.

< Zabura 50 >