< Zabura 50 >
1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
Psaume d'Asaph. Le Dieu fort, Dieu, l'Éternel, a parlé: il a convoqué la terre, Du soleil levant au soleil couchant.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
De Sion, parfaite en beauté, Dieu fait rayonner sa splendeur.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Il vient, notre Dieu, et il ne se tait point; Devant lui est un feu dévorant. Autour de lui une tempête furieuse.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
Il convoque les cieux d'en haut. Ainsi que la terre, pour juger son peuple:
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
«Rassemblez-moi mes fidèles, Qui ont scellé leur alliance avec moi par un sacrifice»
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Et les cieux proclament sa justice; Car c'est Dieu lui-même qui va juger! (Pause)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Écoute, ô mon peuple, et je parlerai. Écoute, ô Israël! Je te ferai entendre mes avertissements: Je suis Dieu, ton Dieu.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Ce n'est pas pour tes sacrifices que je te ferai des reproches, Ni pour tes holocaustes, qui sont continuellement devant moi.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
Je ne prendrai point de taureau dans ta maison, Ni de bouc dans tes bergeries;
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
Car c'est à moi qu'appartiennent tous les animaux des forêts. Ainsi que les bêtes des montagnes, par milliers.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
Je connais tous les oiseaux des montagnes, Et tout ce qui se meut dans les champs m'appartient.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
Si j'avais faim, je ne t'en dirais rien; Car à moi est le monde et tout ce qu'il renferme.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Ai-je besoin de manger la chair des taureaux, Ou de boire le sang des boucs?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Pour sacrifice, offre à Dieu tes louanges, Et accomplis tes voeux envers le Très-Haut!
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
Puis, invoque-moi au jour de la détresse: Je te délivrerai, et tu me glorifieras.
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Mais Dieu dit au méchant: «A quoi bon réciter mes commandements Et célébrer des lèvres mon alliance,
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Quand tu hais la réprimande Et quand tu repousses mes paroles loin de toi?
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
Lorsque tu vois un voleur, tu te plais avec lui; Tu fais cause commune avec les adultères.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Tu livres ta bouche à la calomnie, Et ta langue ourdit la fraude.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Tu t'assieds et tu parles contre ton frère; Tu diffames le fils de ta mère.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
Voilà ce que tu as fait; et parce que j'ai gardé le silence, Tu t'es imaginé que j'étais pareil à toi! Je vais te reprendre et mettre ton iniquité sous tes yeux.»
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Comprenez donc cela, vous qui oubliez Dieu, De peur que je ne vous mette en pièces. Sans que personne puisse vous délivrer!
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Celui qui offre pour sacrifice la louange, me glorifie; Et à celui qui veille sur sa conduite Je ferai contempler le salut de Dieu.