< Zabura 50 >
1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
A Psalm of Asaph. The mighty God, [even] the LORD, hath spoken, and called the earth from the rising to the setting of the sun.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Out of Zion, the perfection of beauty, God hath shined.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Our God shall come, and shall not keep silence: a fire shall devour before him, and it shall be very tempestuous around him.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
He shall call to the heavens from above, and to the earth, that he may judge his people.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
Gather my saints together to me; those that have made a covenant with me by sacrifice.
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
And the heavens shall declare his righteousness: for God [is] judge himself. (Selah)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Hear, O my people, and I will speak; O Israel, and I will testify against thee: I [am] God, [even] thy God.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
I will not reprove thee for thy sacrifices or thy burnt-offerings, [to have been] continually before me.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
I will take no bullock out of thy house, [nor] he-goats out of thy folds.
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
For every beast of the forest [is] mine, [and] the cattle upon a thousand hills.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
I know all the fowls of the mountains: and the wild beasts of the field [are] mine.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
If I were hungry, I would not tell thee: for the world [is] mine, and the fullness thereof.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Will I eat the flesh of bulls, or drink the blood of goats?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Offer to God thanksgiving; and pay thy vows to the Most High:
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
And call upon me in the day of trouble: I will deliver thee, and thou shalt glorify me.
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
But to the wicked God saith, What hast thou to do to declare my statutes, or [that] thou shouldest take my covenant in thy mouth?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Seeing thou hatest instruction, and castest my words behind thee.
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
When thou sawest a thief, then thou consentedst with him, and hast been partaker with adulterers.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Thou givest thy mouth to evil, and thy tongue frameth deceit.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Thou sittest [and] speakest against thy brother; thou slanderest thy own mother's son.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
These [things] hast thou done, and I kept silence; thou thoughtest that I was altogether [such an one] as thyself: [but] I will reprove thee, and set [them] in order before thine eyes.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Now consider this, ye that forget God, lest I tear [you] in pieces, and [there be] none to deliver.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Whoever offereth praise glorifieth me: and to him that ordereth [his] deportment [aright] will I show the salvation of God.