< Zabura 50 >
1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
A Melody of Asaph. El, Elohim, Yahweh, hath spoken, and culled the earth, From the rising of the sun, unto the going in thereof:
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Out of Zion the perfection of beauty, God, hath shone forth.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Let our God come, and let him not keep silence! A fire—before him, shall devour, And, around him, hath it become exceeding tempestuous:
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
He calleth, Unto the heavens above, And unto the earth, That he may judge his people.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
Gather yourselves unto me—ye my men of lovingkindness, Who have solemnised my covenant over sacrifice.
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Now have the heavens declared his righteousness, Because, God, is, about to judge. (Selah)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Hear, O my people, and I will speak, O Israel, and I will adjure thee, God, thine own God, I am: —
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Not, for thy sacrifices, will I reprove thee, Nor for thine ascending-offerings, before me continually:
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
I will not take out of thy house—a bullock, Nor out of thy folds—he-goats;
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
For, mine, is every wild-beast of the forest, The cattle on the mountains, in their thousands;
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
I know every bird of the mountains, And, the moving things of the plain, are with me:
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
If I were hungry, I would not tell thee, For, mine, is the world, and the fulness thereof.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Will I eat the flesh of mighty oxen? Or, the blood of he-goats, will I drink?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Sacrifice to God a thankoffering, And pay to the Most High thy vows;
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
Call upon me, then, in the day of distress, I will deliver thee, that thou mayest glorify me.
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
But, to the lawless one, God saith, What hast, thou, to do, to recount my statutes? Or that thou hast taken up my covenant upon thy mouth?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Seeing that, thou, hast hated correction, And hast cast my words behind thee;
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
If thou sawest a thief, then didst thou run with him, —And, with adulterers, hath been thy chosen life;
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Thy mouth, hast thou thrust into wickedness, And, thy tongue, kept weaving deceit;
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Thou wouldst sit down—Against thine own brother, wouldst thou speak, Against thine own mother’s son, wouldst thou expose a fault: —
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
These things, hast thou done, and I have kept silence, Thou thoughtest that I should really be like thyself, I will convict thee, yea I will set [thine offences] in order before thine eyes.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Understand this, I pray you, ye forgetters of GOD, Lest I tear in pieces, and there be none to deliver: —
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
He that sacrificeth a thankoffering, will glorify me, —And will prepare a way by which I may show him the salvation of God.