< Zabura 50 >

1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
A PSALM OF ASAPH. The God of gods—YHWH—has spoken, And He calls to the earth From the rising of the sun to its going in.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
From Zion, the perfection of beauty, God shone.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Our God comes, and is not silent, Fire devours before Him, And around Him it has been very tempestuous.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
He calls to the heavens from above, And to the earth, to judge His people.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
Gather My saints to Me, Making covenant with Me over a sacrifice.
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
And the heavens declare His righteousness, For God Himself is judging. (Selah)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Hear, O My people, and I speak, O Israel, and I testify against you, God—I [am] your God.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
I do not reprove you for your sacrifices, Indeed, your burnt-offerings [Are] continually before Me.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
I do not take a bullock from your house, [Or] male goats from your folds.
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
For every beast of the forest [is] Mine, The livestock on the hills of oxen.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
I have known every bird of the mountains, And the wild beast of the field [is] with Me.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
If I am hungry I do not tell [it] to you, For the world and its fullness [is] Mine.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Do I eat the flesh of bulls, And drink the blood of male goats?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Sacrifice to God confession, And complete your vows to the Most High.
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
And call Me in a day of adversity, I deliver you, and you honor Me.
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
And to the wicked God has said: What to you—to recount My statutes? That you lift up My covenant on your mouth?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Indeed, you have hated instruction, And cast My words behind you.
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
If you have seen a thief, Then you are pleased with him, And your portion [is] with adulterers.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
You have sent forth your mouth with evil, And your tongue joins deceit together,
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
You sit, you speak against your brother, You give slander against a son of your mother.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
These you did, and I kept silent, You have thought that I am like you, I reprove you, and set in array before your eyes.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Now understand this, You who are forgetting God, Lest I tear, and there is no deliverer.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
He who is sacrificing praise honors Me, As for him who makes a way, I cause him to look on the salvation of God!

< Zabura 50 >