< Zabura 50 >

1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
“A psalm of Assaph.” The God of gods, the Lord, speaketh, and calleth the earth, from the rising of the sun unto his setting.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Out of Zion, the perfection of beauty, God shineth forth.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Our God is coming, and will not keep silence: a fire devoureth before him, and round him there rageth a mighty storm.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
He will call to the heavens above, and to the earth, to judge his people.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
“Gather together unto me my pious servants, who make a covenant with me by sacrifice.”
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
And the heavens tell of his righteousness; for God is judge himself. (Selah)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
“Hear, O my people, and I will speak; O Israel, and I will testify against thee: God, thy God, am I.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Not because of thy sacrifices will I reprove thee; and thy burnt-offerings are continually before me.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
I will not take a bullock out of thy house, nor he-goats out of thy folds.
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
For mine are all the beasts of the forest, the cattle upon a thousand mountains.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
I know all the fowls of the mountains: whatever moveth on the fields is with me.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
If I were hungry, I would not say it to thee; for mine is the world, and what filleth it.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Do I eat the flesh of fatted bulls, or drink the blood of he-goats?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Offer unto God thanksgiving; and pay unto the Most High thy vows;
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
And call on me on the day of distress: I will deliver thee, — and so wilt thou glorify me.”
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
But unto the wicked God saith, “What hast thou to do to relate my statutes, and why bearest thou my covenant upon thy mouth?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
And yet thou hatest instruction, and castest my words behind thee.
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
When thou seest a thief, then art thou pleased with him, and with adulterers hast thou thy portion.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Thou lettest loose thy mouth with evil, and thy tongue frameth deceit.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Thou sittest and speakest against thy brother; against thy own mother's son thou utterest slander.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
These things hast thou done, and I kept silence: thou didst ween that I am like thyself; [but] I will reprove thee, and set it in order before thy eyes.”
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Do but reflect on this, ye that forget God, lest I tear [you] in pieces, with none to deliver.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Whoso offereth thanksgiving glorifieth me: and to him that ordereth his course aright, will I show the salvation of God.

< Zabura 50 >