< Zabura 50 >
1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
A Psalme of Asaph. The God of Gods, euen the Lord hath spoken and called the earth from the rising vp of the sunne vnto the going downe thereof.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Out of Zion, which is the perfection of beautie, hath God shined.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Our God shall come and shall not keepe silence: a fire shall deuoure before him, and a mightie tempest shall be mooued round about him.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
Hee shall call the heauen aboue, and the earth to iudge his people.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
Gather my Saints together vnto me, those that make a couenant with me with sacrifice.
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
And the heauens shall declare his righteousnes: for God is iudge himselfe. (Selah)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Heare, O my people, and I wil speake: heare, O Israel, and I wil testifie vnto thee: for I am God, euen thy God.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
I wil not reproue thee for thy sacrifices, or thy burnt offerings, that haue not bene continually before me.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
I will take no bullocke out of thine house, nor goates out of thy foldes.
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
For all the beastes of the forest are mine, and the beastes on a thousand mountaines.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
I knowe all the foules on the mountaines: and the wilde beastes of the fielde are mine.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
If I bee hungry, I will not tell thee: for the world is mine, and all that therein is.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Will I eate the flesh of bulles? or drinke the blood of goates?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Offer vnto God praise, and pay thy vowes vnto the most High,
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
And call vpon me in the day of trouble: so will I deliuer thee, and thou shalt glorifie me.
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
But vnto the wicked said God, What hast thou to doe to declare mine ordinances, that thou shouldest take my couenant in thy mouth,
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Seeing thou hatest to bee reformed, and hast cast my wordes behinde thee?
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
For when thou seest a thiefe, thou runnest with him, and thou art partaker with the adulterers.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Thou giuest thy mouth to euill, and with thy tongue thou forgest deceit.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Thou sittest, and speakest against thy brother, and slanderest thy mothers sonne.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
These things hast thou done, and I held my tongue: therefore thou thoughtest that I was like thee: but I will reproue thee, and set them in order before thee.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Oh cosider this, ye that forget God, least I teare you in pieces, and there be none that can deliuer you.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
He that offereth praise, shall glorifie mee: and to him, that disposeth his way aright, will I shew the saluation of God.