< Zabura 50 >
1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
A Psalm. Of Asaph. God, Elohim-Jehovah, hath spoken, and called the earth from the rising of the sun unto the going down thereof.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Out of Zion, the perfection of beauty, God hath shined forth.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Our God will come, and will not keep silence: fire shall devour before him, and it shall be very tempestuous round about him.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
He will call to the heavens from above, and to the earth, that he may judge his people:
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
Gather unto me my godly ones, those that have made a covenant with me by sacrifice!
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
And the heavens shall declare his righteousness; for God executeth judgment himself. (Selah)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Hear, my people, and I will speak; O Israel, and I will testify unto thee: I am God, thy God.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
I will not reprove thee for thy sacrifices, or thy burnt-offerings, continually before me;
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
I will take no bullock out of thy house, [nor] he-goats out of thy folds:
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
For every beast of the forest is mine, the cattle upon a thousand hills;
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
I know all the fowl of the mountains, and the roaming creatures of the field are mine:
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
If I were hungry, I would not tell thee; for the world is mine, and the fulness thereof.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Should I eat the flesh of bulls, and drink the blood of goats?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Offer unto God thanksgiving, and perform thy vows unto the Most High;
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
And call upon me in the day of trouble; I will deliver thee, and thou shalt glorify me.
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
But unto the wicked God saith, What hast thou to do to declare my statutes, or that thou shouldest take my covenant into thy mouth,
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Seeing thou hast hated correction and hast cast my words behind thee?
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
When thou sawest a thief, thou didst take pleasure in him, and thy portion was with adulterers;
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Thou lettest thy mouth loose to evil, and thy tongue frameth deceit;
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Thou sittest [and] speakest against thy brother, thou revilest thine own mother's son:
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
These [things] hast thou done, and I kept silence; thou thoughtest that I was altogether as thyself: [but] I will reprove thee, and set [them] in order before thine eyes.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Now consider this, ye that forget God, lest I tear in pieces, and there be no deliverer.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Whoso offereth praise glorifieth me; and to him that ordereth [his] way will I shew the salvation of God.