< Zabura 50 >
1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
(En salme af Asaf.) Gud, Gud HERREN talede og stævnede Jorden hid fra Sol i Opgang til Sol i Bjærge;
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
fra Zion, Skønhedens Krone, viste Gud sig i Stråleglans
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
vor Gud komme og tie ikke! - Foran ham gik fortærende Ild, omkring ham rasede Storm;
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
han stævnede Himlen deroppe hid og Jorden for at dømme sit Folk:
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
"Saml mig mine fromme, der sluttede Pagt med mig ved Ofre!"
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Og Himlen forkyndte hans Retfærd, at Gud er den, der dømmer. (Sela)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Hør, mit Folk, jeg vil tale, Israel, jeg vil vidne imod dig, Gud, din Gud er jeg!
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Jeg laster dig ikke for dine Slagtofre, dine Brændofre har jeg jo stadig for Øje;
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
jeg tager ej Tyre fra dit Hus eller Bukke fra dine Stalde;
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
thi mig tilhører alt Skovens Vildt, Dyrene på de tusinde Bjerge;
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
jeg kender alle Bjergenes Fugle, har rede på Markens Vrimmel.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
Om jeg hungred, jeg sagde det ikke til dig, thi mit er Jorderig og dets Fylde!
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Mon jeg æder Tyres Kød eller drikker Bukkes Blod?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Lovsang skal du ofre til Gud og holde den Højeste dine Løfter.
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
Og kald på mig på Nødens Dag; jeg vil udfri dig, og du skal ære mig,
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Men til Den gudløse siger Gud: Hvi regner du op mine Bud og fører min Pagt i Munden,
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
når du dog hader Tugt og kaster mine Ord bag din Ryg?
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
Ser du en Tyv, slår du Følge med ham, med Horkarle bolder du til,
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
slipper Munden løs med ondt, din Tunge bærer på Svig.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Du sidder og skænder din Broder, bagtaler din Moders Søn;
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
det gør du, og jeg skulde tie, og du skulde tænke, jeg er som du! Revse dig vil jeg og gøre dig det klart.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Mærk jer det, I, som glemmer Gud, at jeg ikke skal rive jer redningsløst sønder.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Den, der ofrer Taksigelse, ærer mig; den, der agter på Vejen, lader jeg se Guds Frelse.