< Zabura 50 >

1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
En Psalme af Asaf. Den Almægtige, Gud Herren har talt og kaldet ad Jorden, fra Solens Opgang indtil dens Nedgang.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
Fra Zion, Skønhedens Krone, aabenbarede Gud sig herligt.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Vor Gud skal komme og ikke tie; en Ild for hans Ansigt skal fortære, og omkring ham stormer det saare.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
Han kalder ad Himmelen oventil og ad Jorden for at dømme sit Folk.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
„Samler mig mine hellige, som have sluttet Pagt med mig ved Offer”.
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
Og Himlene kundgjorde hans Retfærdighed; thi Gud, han er Dommer. (Sela)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
Hør, mit Folk, og jeg vil tale; Israel! og jeg vil vidne imod dig; jeg er Gud, din Gud.
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
Jeg vil ikke gaa i Rette med dig for dine Slagtofre og for dine Brændofre, som ere altid for mig.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
Jeg vil ikke tage en Okse af dit Hus, ej heller Bukke af dine Stalde.
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
Thi alle Dyrene i Skoven høre mig til, Dyrene paa Bjergene i Tusindtal.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
Jeg kender alle Fuglene paa Bjergene, og hvad der vrimler paa Marken, er hos mig.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
Dersom jeg hungrede, vilde jeg ikke sige dig det; thi Jorderige hører mig til og dets Fylde.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Skulde jeg vel æde Oksers Kød eller drikke Bukkes Blod?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Offer Gud Taksigelse og betal den Højeste dine Løfter!
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
Og kald paa mig paa Nødens Dag; jeg vil udfri dig, og du skal ære mig.
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Men til den ugudelige siger Gud: Hvad kommer det dig ved at tale om mine Skikke og at tage min Pagt i din Mund,
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
da du dog hader Tugt og kaster mine Ord bag dig?
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
Dersom du ser en Tyv, da er du Ven med ham, og med Horkarle er din Del.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
Du skikker din Mund til ondt, og med din Tunge digter du Svig.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
Du sidder og taler imod din Broder, du sætter Klik paa din Moders Søn.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
Disse Ting har du gjort, og jeg har tiet; du har tænkt, at jeg vel var som du; men jeg vil straffe dig og stille det frem for dine Øjne.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Forstaar dog dette, I, som have glemt Gud! at jeg ikke skal rive bort, og der ingen er, som frier.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
Den, som ofrer Taksigelse, han ærer mig, og den, som agter paa Vejen, ham vil jeg lade se Guds Frelse.

< Zabura 50 >