< Zabura 5 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Busa. Ta Dawuda. Ka saurare kalmomina, ya Ubangiji, ka ji ajiyar zuciyata.
برای رهبر سرایندگان: مزمور داوود، با همراهی سازهای بادی. ای خداوند، به سخنان من گوش بده و به نالهٔ من توجه فرما.
2 Ka saurare kukata na neman taimako, Sarkina da Allahna, gama gare ka nake addu’a.
ای پادشاه و ای خدای من، به فریادم برس، زیرا من فقط نزد تو دعا می‌کنم.
3 Da safe, ya Ubangiji, ka ji muryata; da safe na gabatar da bukatuna a gabanka in kuma jira da sa zuciya.
ای خداوند، صبحگاهان به پیشگاه تو دعا می‌کنم و تو صدای مرا می‌شنوی، پس من انتظار خواهم کشید تا جواب مرا بدهی.
4 Kai ba Allahn da yake jin daɗin mugu ba ne; gama kana gāba da dukan masu aikata mugunta.
تو خدایی نیستی که گناه را دوست بداری و شرارت را تحمل کنی.
5 Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.
تو تحمل دیدن متکبران را نداری و از همهٔ بدکاران نفرت داری.
6 Kakan hallaka masu yin ƙarya. Masu kisankai da mutane masu ruɗu Ubangiji yana ƙyama.
ای خداوند، تو از قاتلان و حیله‌گران بیزاری و دروغگویان را هلاک می‌کنی.
7 Amma ni, ta wurin jinƙanka mai girma, zan shiga gidanka; da bangirma zan durƙusa ga haikalinka.
اما من در پناه محبت عظیم تو به خانهٔ مقدّست داخل خواهم شد و با ترس و احترام، تو را عبادت خواهم کرد.
8 Ka bi da ni, ya Ubangiji, cikin adalcinka saboda abokan gābana, ka fayyace hanyarka a gabana.
ای خداوند عادل، راه خود را به من نشان ده و مرا هدایت نما تا دشمنانم نتوانند بر من چیره شوند.
9 Babu ko kalma guda daga bakinsu da za a dogara da ita; marmarinsu kawai shi ne su hallakar da waɗansu. Maƙogwaronsu buɗaɗɗen kabari ne; da harshensu suna faɗin ƙarya.
به سخنان دهانشان نمی‌توان اعتماد کرد و دلشان مملو از شرارت است. گلویشان گوری است گشاده، و دروغ بر زبانشان است.
10 Ka furta su masu laifi, ya Allah! Bari makircinsu yă zama fāɗuwarsu. Ka kore su saboda yawan zunubansu, saboda sun tayar maka.
ای خدا، تو آنها را محکوم کن و بگذار خود در دامهایشان گرفتار شوند! آنها را دور بینداز، زیرا گناهان زیادی مرتکب شده‌اند و بر ضد تو برخاسته‌اند.
11 Amma bari dukan waɗanda suke neman mafaka gare ka su yi murna; bari kullum su yi ta rerawa saboda farin ciki. Ka buɗe kāriyarka a bisansu, domin waɗanda suke ƙaunar sunanka su yi farin ciki a cikinka.
اما بگذار همهٔ کسانی که به تو پناه می‌آورند، خوشحال شوند و همیشه با شادی سرود بخوانند. از کسانی که تو را دوست دارند محافظت نما تا آنها در پناه تو شادمان باشند.
12 Gama tabbatacce, ya Ubangiji, kakan albarkaci adalai; kakan kewaye su da tagomashinka kamar garkuwa.
تو ای خداوند، عادلان را برکت می‌دهی و ایشان را با سپر محبت خود محافظت می‌نمایی.

< Zabura 5 >