< Zabura 5 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Busa. Ta Dawuda. Ka saurare kalmomina, ya Ubangiji, ka ji ajiyar zuciyata.
Dāvida dziesma. Dziedātāju vadonim uz stabulēm. Ak Kungs, klausies uz maniem vārdiem, ņem vērā manas domas.
2 Ka saurare kukata na neman taimako, Sarkina da Allahna, gama gare ka nake addu’a.
Samani manas kliegšanas balsi, mans ķēniņ un mans Dievs, jo es Tevi gribu pielūgt.
3 Da safe, ya Ubangiji, ka ji muryata; da safe na gabatar da bukatuna a gabanka in kuma jira da sa zuciya.
Rītos, ak Kungs, klausi manu balsi, rītos es uz Tevi gribu sataisīties un skatīties.
4 Kai ba Allahn da yake jin daɗin mugu ba ne; gama kana gāba da dukan masu aikata mugunta.
Jo Tu neesi tāds Dievs, kam bezdievība patīk; kas ir ļauns, tas pie Tevis nepaliek.
5 Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.
Trakotāji nepastāvēs priekš Tavām acīm, Tu ienīsti visus ļauna darītājus.
6 Kakan hallaka masu yin ƙarya. Masu kisankai da mutane masu ruɗu Ubangiji yana ƙyama.
Tu nomaitā melkuļus, asins vainīgie un viltnieki Tam Kungam ir negantība.
7 Amma ni, ta wurin jinƙanka mai girma, zan shiga gidanka; da bangirma zan durƙusa ga haikalinka.
Bet es iešu Tavā namā caur Tavu lielo žēlastību, es pielūgšu Tava svētuma mājoklī, Tevi bīdamies.
8 Ka bi da ni, ya Ubangiji, cikin adalcinka saboda abokan gābana, ka fayyace hanyarka a gabana.
Kungs, vadi mani pēc Savas taisnības, manu glūnētāju dēļ, dari līdzenu Savu ceļu manā priekšā.
9 Babu ko kalma guda daga bakinsu da za a dogara da ita; marmarinsu kawai shi ne su hallakar da waɗansu. Maƙogwaronsu buɗaɗɗen kabari ne; da harshensu suna faɗin ƙarya.
Jo viņu mutē nav nekādas patiesības, viņu sirdīs ir ļaunums, viņu rīkle ir atvērts kaps, ar savu mēli tie glauda.
10 Ka furta su masu laifi, ya Allah! Bari makircinsu yă zama fāɗuwarsu. Ka kore su saboda yawan zunubansu, saboda sun tayar maka.
Sodi tos, ak Dievs, lai tie krīt no saviem padomiem; atstum tos viņu lielos noziegumos, jo tie pret Tevi sacēlušies,
11 Amma bari dukan waɗanda suke neman mafaka gare ka su yi murna; bari kullum su yi ta rerawa saboda farin ciki. Ka buɗe kāriyarka a bisansu, domin waɗanda suke ƙaunar sunanka su yi farin ciki a cikinka.
Bet lai priecājās visi, kas uz Tevi cerē, mūžīgi lai tie gavilē, jo Tu tos pasargi; lai līksmojās iekš Tevis, kas Tavu vārdu mīļo.
12 Gama tabbatacce, ya Ubangiji, kakan albarkaci adalai; kakan kewaye su da tagomashinka kamar garkuwa.
Jo Tu, Kungs, svētīsi to taisno, un to pušķosi ar žēlastību kā ar bruņām.

< Zabura 5 >