< Zabura 5 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Busa. Ta Dawuda. Ka saurare kalmomina, ya Ubangiji, ka ji ajiyar zuciyata.
Yahweh, listen to me while I pray! Pay attention to me when I am groaning [because I am suffering very much].
2 Ka saurare kukata na neman taimako, Sarkina da Allahna, gama gare ka nake addu’a.
You are my King and my God. When I call to you to ask you to help me, listen to me, because you are the one to whom I pray.
3 Da safe, ya Ubangiji, ka ji muryata; da safe na gabatar da bukatuna a gabanka in kuma jira da sa zuciya.
Listen to me when I pray to you [each] morning, and I wait for you to reply.
4 Kai ba Allahn da yake jin daɗin mugu ba ne; gama kana gāba da dukan masu aikata mugunta.
You are not a god who is pleased with wicked people; you do not (associate with/invite into your house) [those who do what is] evil.
5 Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.
You do not allow those who are very proud to come to you to worship you. You hate all those who do evil things.
6 Kakan hallaka masu yin ƙarya. Masu kisankai da mutane masu ruɗu Ubangiji yana ƙyama.
You get rid of liars, and you despise those who murder [others] and those who deceive [others].
7 Amma ni, ta wurin jinƙanka mai girma, zan shiga gidanka; da bangirma zan durƙusa ga haikalinka.
Yahweh, because you love me so much and so faithfully, I come into your temple. I revere you greatly, and I bow down to worship you at your sacred temple.
8 Ka bi da ni, ya Ubangiji, cikin adalcinka saboda abokan gābana, ka fayyace hanyarka a gabana.
Yahweh, because you act righteously toward me, show me what is right for me to do. Because I have many enemies, show me clearly what you want me to do.
9 Babu ko kalma guda daga bakinsu da za a dogara da ita; marmarinsu kawai shi ne su hallakar da waɗansu. Maƙogwaronsu buɗaɗɗen kabari ne; da harshensu suna faɗin ƙarya.
My enemies never say what is true; they just want to destroy [others]. The things that they say [MTY] are [as foul as] an open grave [where a corpse is decaying]. They use their tongues to tell lies.
10 Ka furta su masu laifi, ya Allah! Bari makircinsu yă zama fāɗuwarsu. Ka kore su saboda yawan zunubansu, saboda sun tayar maka.
O God, declare that they are guilty [MTY] [and punish them]. Cause them to experience the same disasters/troubles that they plan to cause to happen to others. Get rid of them because they have committed many sins, and they have rebelled against you.
11 Amma bari dukan waɗanda suke neman mafaka gare ka su yi murna; bari kullum su yi ta rerawa saboda farin ciki. Ka buɗe kāriyarka a bisansu, domin waɗanda suke ƙaunar sunanka su yi farin ciki a cikinka.
But cause that all those who go to you to be protected will rejoice; cause them to sing joyfully to you forever. Protect those who love you [MTY]; they are truly happy because (of what you [do for them/they belong to] you).
12 Gama tabbatacce, ya Ubangiji, kakan albarkaci adalai; kakan kewaye su da tagomashinka kamar garkuwa.
Yahweh, you always bless those who act righteously; you protect them like a [soldier is protected by his] shield [SIM].

< Zabura 5 >