< Zabura 5 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Busa. Ta Dawuda. Ka saurare kalmomina, ya Ubangiji, ka ji ajiyar zuciyata.
For the leader: A psalm of David, to be accompanied by the flute. Hear my words, Lord: give heed to my whisper.
2 Ka saurare kukata na neman taimako, Sarkina da Allahna, gama gare ka nake addu’a.
Attend to my loud cry for help, my king and my God.
3 Da safe, ya Ubangiji, ka ji muryata; da safe na gabatar da bukatuna a gabanka in kuma jira da sa zuciya.
When I pray to you, Lord, in the morning, hear my voice. I make ready for you in the morning, and look for a sign.
4 Kai ba Allahn da yake jin daɗin mugu ba ne; gama kana gāba da dukan masu aikata mugunta.
For you are no God who takes pleasure in wickedness: no one of evil can be your guest.
5 Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.
No braggarts can stand in your presence, you hate all workers of wrong.
6 Kakan hallaka masu yin ƙarya. Masu kisankai da mutane masu ruɗu Ubangiji yana ƙyama.
You destroy all speakers of lies, people of blood and deceit you abhor.
7 Amma ni, ta wurin jinƙanka mai girma, zan shiga gidanka; da bangirma zan durƙusa ga haikalinka.
But I, through your kindness abundant, may enter your house, and towards the shrine of your temple may reverently bow.
8 Ka bi da ni, ya Ubangiji, cikin adalcinka saboda abokan gābana, ka fayyace hanyarka a gabana.
Lead me, Lord, in your righteousness because of my enemies. Make your way level before me.
9 Babu ko kalma guda daga bakinsu da za a dogara da ita; marmarinsu kawai shi ne su hallakar da waɗansu. Maƙogwaronsu buɗaɗɗen kabari ne; da harshensu suna faɗin ƙarya.
For their mouth is a stranger to truth, their heart is a pit of destruction. Their throat is a wide open grave, their tongue the smooth tongue of the hypocrite.
10 Ka furta su masu laifi, ya Allah! Bari makircinsu yă zama fāɗuwarsu. Ka kore su saboda yawan zunubansu, saboda sun tayar maka.
Condemn them, God; let their schemes bring them down to the ground. For their numberless crimes thrust them down for playing the rebel against you.
11 Amma bari dukan waɗanda suke neman mafaka gare ka su yi murna; bari kullum su yi ta rerawa saboda farin ciki. Ka buɗe kāriyarka a bisansu, domin waɗanda suke ƙaunar sunanka su yi farin ciki a cikinka.
But let all who take refuge in you ring out their gladness forever. Protect those who love your name, so they may exult in you.
12 Gama tabbatacce, ya Ubangiji, kakan albarkaci adalai; kakan kewaye su da tagomashinka kamar garkuwa.
For you give your blessing, Lord, to the godly, and the shield of your favor protects them.

< Zabura 5 >