< Zabura 5 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Busa. Ta Dawuda. Ka saurare kalmomina, ya Ubangiji, ka ji ajiyar zuciyata.
TO THE OVERSEER. [BLOWN] INTO THE PIPES. A PSALM OF DAVID. Hear my sayings, O YHWH, Consider my (meditation)
2 Ka saurare kukata na neman taimako, Sarkina da Allahna, gama gare ka nake addu’a.
Be attentive to the voice of my cry, My King and my God, For I pray to You habitually.
3 Da safe, ya Ubangiji, ka ji muryata; da safe na gabatar da bukatuna a gabanka in kuma jira da sa zuciya.
YHWH, [in] the morning You hear my voice, [In] the morning I set in array for You, And I look out [expectantly].
4 Kai ba Allahn da yake jin daɗin mugu ba ne; gama kana gāba da dukan masu aikata mugunta.
For You [are] not a God desiring wickedness, Evil does not inhabit You.
5 Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.
The boastful do not station themselves before Your eyes: You have hated all working iniquity.
6 Kakan hallaka masu yin ƙarya. Masu kisankai da mutane masu ruɗu Ubangiji yana ƙyama.
You destroy those speaking lies, YHWH detests a man of blood and deceit.
7 Amma ni, ta wurin jinƙanka mai girma, zan shiga gidanka; da bangirma zan durƙusa ga haikalinka.
And I, in the abundance of Your kindness, I enter Your house, I bow myself toward Your holy temple in Your fear.
8 Ka bi da ni, ya Ubangiji, cikin adalcinka saboda abokan gābana, ka fayyace hanyarka a gabana.
O YHWH, lead me in Your righteousness, Because of those observing me, Make Your way straight before me,
9 Babu ko kalma guda daga bakinsu da za a dogara da ita; marmarinsu kawai shi ne su hallakar da waɗansu. Maƙogwaronsu buɗaɗɗen kabari ne; da harshensu suna faɗin ƙarya.
For there is no stability in their mouth. Their heart [is] mischiefs, Their throat [is] an open grave, They make their tongue smooth.
10 Ka furta su masu laifi, ya Allah! Bari makircinsu yă zama fāɗuwarsu. Ka kore su saboda yawan zunubansu, saboda sun tayar maka.
Declare them guilty, O God, Let them fall from their own counsels, In the abundance of their transgressions Drive them away, Because they have been rebellious against You.
11 Amma bari dukan waɗanda suke neman mafaka gare ka su yi murna; bari kullum su yi ta rerawa saboda farin ciki. Ka buɗe kāriyarka a bisansu, domin waɗanda suke ƙaunar sunanka su yi farin ciki a cikinka.
And all trusting in You rejoice, They sing for all time, and You cover them over, And those loving Your Name exult in You.
12 Gama tabbatacce, ya Ubangiji, kakan albarkaci adalai; kakan kewaye su da tagomashinka kamar garkuwa.
For You bless the righteous, O YHWH, Surrounding him with favor as a buckler!

< Zabura 5 >