< Zabura 5 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Busa. Ta Dawuda. Ka saurare kalmomina, ya Ubangiji, ka ji ajiyar zuciyata.
For the end, a Psalm of David, concerning her that inherits. Hearken to my words, O Lord, attend to my cry.
2 Ka saurare kukata na neman taimako, Sarkina da Allahna, gama gare ka nake addu’a.
Attend to the voice of my supplication, my King, and my God: for to thee, O Lord, will I pray.
3 Da safe, ya Ubangiji, ka ji muryata; da safe na gabatar da bukatuna a gabanka in kuma jira da sa zuciya.
In the morning thou shalt hear my voice: in the morning will I wait upon thee, and will look up.
4 Kai ba Allahn da yake jin daɗin mugu ba ne; gama kana gāba da dukan masu aikata mugunta.
For thou art not a god that desires iniquity; neither shall the worker of wickedness dwell with thee.
5 Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.
Neither shall the transgressors continue in thy sight: thou hatest, O Lord, all them that work iniquity.
6 Kakan hallaka masu yin ƙarya. Masu kisankai da mutane masu ruɗu Ubangiji yana ƙyama.
Thou wilt destroy all that speak falsehood: the Lord abhors the bloody and deceitful man.
7 Amma ni, ta wurin jinƙanka mai girma, zan shiga gidanka; da bangirma zan durƙusa ga haikalinka.
But I will enter into thine house in the multitude of thy mercy: I will worship in thy fear toward thy holy temple.
8 Ka bi da ni, ya Ubangiji, cikin adalcinka saboda abokan gābana, ka fayyace hanyarka a gabana.
Lead me, O Lord, in thy righteousness because of mine enemies; make my way plain before thy face.
9 Babu ko kalma guda daga bakinsu da za a dogara da ita; marmarinsu kawai shi ne su hallakar da waɗansu. Maƙogwaronsu buɗaɗɗen kabari ne; da harshensu suna faɗin ƙarya.
For there is no truth in their mouth; their heart is vain; their throat is an open sepulchre; with their tongues they have used deceit.
10 Ka furta su masu laifi, ya Allah! Bari makircinsu yă zama fāɗuwarsu. Ka kore su saboda yawan zunubansu, saboda sun tayar maka.
Judge them, O God; let them fail of their counsels: cast them out according to the abundance of their ungodliness; for they have provoked thee, O Lord.
11 Amma bari dukan waɗanda suke neman mafaka gare ka su yi murna; bari kullum su yi ta rerawa saboda farin ciki. Ka buɗe kāriyarka a bisansu, domin waɗanda suke ƙaunar sunanka su yi farin ciki a cikinka.
But let all that trust on thee be glad in thee: they shall exult for ever, and thou shalt dwell among them; and all that love thy name shall rejoice in thee.
12 Gama tabbatacce, ya Ubangiji, kakan albarkaci adalai; kakan kewaye su da tagomashinka kamar garkuwa.
For thou, Lord, shalt bless the righteous: thou hast compassed us as with a shield of favour.

< Zabura 5 >