< Zabura 49 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
En Psalm, till att föresjunga, Korah barnas. Hörer till, all folk; akter häruppå, alle I, som på denna tid lefven;
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
Både den menige man och herrar, både rike och fattige; den ene med den andra.
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
Min mun skall tala vishet, och mitt hjerta förstånd.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
Vi vilje ett godt ordspråk höra, och en skön dikt på harpo spela.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Hvi skulle jag frukta mig i de onda dagar, när mina förtryckares ondska omfattar mig?
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
Hvilke sig förlåta uppå sitt gods, och trotsa uppå sina stora rikedomar.
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
Kan dock en broder ingen förlösa, eller Gudi någon försona;
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
Ty det kostar för mycket att förlösa deras själ; så att han måste låta det bestå evinnerliga;
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
Om han ock än länge lefver, och grafvena icke ser.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
Ty man skall se, att sådana vise dock dö, så väl som de dårar och galne förgås, och måste låta sitt gods androm.
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
Med deras tankar står det alltså: Deras hus vara förutan ända, deras boningar blifva ifrå slägte till slägte, och de hafva stora äro på jordene.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Likväl kunna de icke blifva i sådana värdighet; utan måste hädan såsom fä.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
Denna deras handel är allsamman galenskap; likväl lofva det deras efterkommande med sin mun. (Sela)
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol )
De ligga i helvete såsom får, döden gnager dem; men de fromme skola hasteliga få råda öfver dem, och deras trotsan måste förgås; uti helvete måste de blifva. (Sheol )
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol )
Men Gud skall förlösa mina själ utu helvetes våld; ty han hafver upptagit mig. (Sela) (Sheol )
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Sköt der intet om, när en rik varder, om hans huses härlighet stor varder;
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
Ty han skall i sin dödstid intet med sig taga, och hans härlighet far intet efter honom;
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Utan han tröstar på detta goda lefvandet, och prisar det, när en gör sig goda dagar.
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
Så fara de efter sina fäder, och få aldrig se ljuset.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Korteliga: När en menniska är i värdighet, och hafver icke förstånd, så far hon hädan såsom fä.