< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
Presten atención a esto, todos ustedes pueblos; deja que tus oídos escuchen esto, todos ustedes que viven en el mundo.
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
Alto y bajo juntos, los pobres y aquellos que tienen riqueza.
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
De mi boca saldrán palabras de sabiduría; y de los pensamientos de mi corazón sabiduría.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
Inclinaré al proverbio mi oído; y diré mi secreto al son del arpa.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
¿Por qué tengo miedo en los días del mal, cuando la maldad de los que maquinan contra mi. me rodeare?
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
Incluso de aquellos cuya confianza está en sus riquezas, y cuyos corazones se enaltecen por sus riquezas.
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
En verdad, nadie puede recuperar su alma por un precio, ni darle a Dios el pago por sí mismo;
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
(Porque toma un gran precio mantener su alma alejada de la muerte, y el hombre no puede dársela).
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
Para que él tenga vida eterna, y nunca vea el inframundo.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
Porque él ve que los sabios llegan a su fin, y las personas necias e insensatas vienen a la destrucción juntas, dejando que su riqueza vaya a otros.
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
El lugar de los muertos es su casa para siempre, y su lugar de reposo por todas las generaciones; aquellos que vienen después de ellos dan sus nombres a sus tierras.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Pero el hombre, como los animales, no continúa para siempre; él llega a su fin como las bestias.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
Este es el camino de los necios; su plata es para aquellos que vienen después de ellos, y sus hijos obtienen el placer de su oro. (Selah)
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
La muerte les dará su alimento como ovejas; el inframundo es su destino y descenderán a él; cuando llegue la mañana los buenos triunfarán sobre ellos; su carne es alimento para gusanos; su forma se desperdicia; el inframundo es su lugar de descanso para siempre. (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
Pero Dios recuperará mi alma; porque él me sacará del poder de la muerte. (Selah) (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
No tengas miedo cuando la riqueza viene a un hombre, y la gloria de su casa se incrementa;
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
Porque a su muerte, él no se llevará nada; su gloria no bajará después de él.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Aunque él pueda tener orgullo en su alma en su tiempo de vida, y los hombres le den alabanza cuando prospera.
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
Él irá a la generación de sus padres; él no verá la luz otra vez.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
El hombre sin entendimiento. como los animales, no continúa para siempre; él llega a su fin como las bestias.

< Zabura 49 >