< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
Ouvi isto, vós todos os povos; inclinae os ouvidos, todos os moradores do mundo,
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
Tanto baixos como altos, tanto ricos como pobres.
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
A minha bocca fallará de sabedoria; e a meditação do meu coração será de entendimento.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
Inclinarei os meus ouvidos a uma parabola: declararei o meu enigma na harpa.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Porque temerei eu nos dias maus, quando me cercar a iniquidade dos que me armam ciladas?
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
Aquelles que confiam na sua fazenda, e se gloriam na multidão das suas riquezas,
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
Nenhum d'elles de modo algum pode remir a seu irmão, ou dar a Deus o resgate d'elle
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
(Pois a redempção da sua alma é carissima, e cessará para sempre);
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
Para que viva para sempre, e não veja corrupção:
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
Porque elle vê que os sabios morrem: perecem egualmente tanto o louco como o brutal, e deixam a outros os seus bens.
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
O seu pensamento interior é que as suas casas serão perpetuas e as suas habitações de geração em geração: dão ás suas terras os seus proprios nomes.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Todavia o homem que está na honra não permanece; antes é como os brutos que perecem.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
Este caminho d'elles é a sua loucura; comtudo a sua posteridade approva as suas palavras (Selah)
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
Como ovelhas são postos na sepultura; a morte se alimentará d'elles; e os rectos terão dominio sobre elles na manhã, e a sua formosura na sepultura se consumirá da sua morada. (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
Mas Deus remirá a minha alma do poder da sepultura, pois me receberá (Selah) (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Não temas, quando alguem se enriquece, quando a gloria da sua casa se engrandece.
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
Porque, quando morrer, nada levará comsigo, nem a sua gloria o acompanhará.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Ainda que na sua vida elle bemdisse a sua alma, e os homens te louvam, quando fizeres bem a ti mesmo,
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
Irá para a geração de seus paes; elles nunca verão a luz
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
O homem que está na honra, e não tem entendimento, é similhante ás bestas que perecem.

< Zabura 49 >