< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
למנצח לבני קרח מזמור שמעו זאת כל העמים האזינו כל ישבי חלד׃
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
גם בני אדם גם בני איש יחד עשיר ואביון׃
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
פי ידבר חכמות והגות לבי תבונות׃
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
אטה למשל אזני אפתח בכנור חידתי׃
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
למה אירא בימי רע עון עקבי יסובני׃
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
הבטחים על חילם וברב עשרם יתהללו׃
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
אח לא פדה יפדה איש לא יתן לאלהים כפרו׃
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
ויקר פדיון נפשם וחדל לעולם׃
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
ויחי עוד לנצח לא יראה השחת׃
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
כי יראה חכמים ימותו יחד כסיל ובער יאבדו ועזבו לאחרים חילם׃
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
קרבם בתימו לעולם משכנתם לדר ודר קראו בשמותם עלי אדמות׃
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
ואדם ביקר בל ילין נמשל כבהמות נדמו׃
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
זה דרכם כסל למו ואחריהם בפיהם ירצו סלה׃
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
כצאן לשאול שתו מות ירעם וירדו בם ישרים לבקר וצירם לבלות שאול מזבל לו׃ (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
אך אלהים יפדה נפשי מיד שאול כי יקחני סלה׃ (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
אל תירא כי יעשר איש כי ירבה כבוד ביתו׃
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
כי לא במותו יקח הכל לא ירד אחריו כבודו׃
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
כי נפשו בחייו יברך ויודך כי תיטיב לך׃
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
תבוא עד דור אבותיו עד נצח לא יראו אור׃
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
אדם ביקר ולא יבין נמשל כבהמות נדמו׃

< Zabura 49 >