< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
Pour la fin, aux fils de Coré, psaume. Écoutez ces choses, vous toutes, nations: prêtez l’oreille, vous qui habitez l’univers;
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
Vous tous, fils de la terre, et fils des hommes, ensemble et de concert, riche et pauvre.
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
Ma bouche parlera sagesse, et la méditation de mon cœur, prudence.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
J’inclinerai mon oreille à une parabole, et je révélerai sur le psaltérion mon sujet.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Pourquoi craindrai-je au jour mauvais? Je craindrai si l’iniquité de ma voie m’environne.
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
Qu’ils craignent ceux qui se confient dans leur puissance, et se glorifient dans l’abondance de leurs richesses.
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
Un frère ne rachète pas son frère: un homme étranger le rachètera-t-il? il ne donnera pas à Dieu de quoi l’apaiser pour lui-même,
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
Ni le prix du rachat de son âme: et il travaillera éternellement.
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
Et il vivra encore jusqu’à la fin.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
Il ne verra pas la mort, lorsqu’il aura vu les sages mourir: l’insensé et le fou périront également. Et ils laisseront à des étrangers leurs richesses.
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
Et leurs sépulcres seront leurs maisons pour toujours. Et leurs tabernacles dans chaque génération; quoiqu’ils aient donné leurs noms à leurs terres.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Et l’homme, lorsqu’il était en honneur, ne l’a pas compris: il a été comparé aux animaux sans raison, et il est devenu semblable à eux.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
Cette voie qu’ils suivent est une pierre d’achoppement pour eux-mêmes, et néanmoins dans la suite ils se complairont dans leurs discours.
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
Comme des brebis, ils ont été parqués dans l’enfer: c’est la mort qui les paîtra. (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
Mais cependant Dieu rachètera mon âme de la main de l’enfer, quand il m’aura pris sous sa protection. (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Ne craignez pas lorsqu’un homme sera devenu riche, et que la gloire de sa maison se sera accrue.
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
Parce que, lorsqu’il sera mort, il n’emportera pas tous ses biens; et que sa gloire ne descendra pas avec lui.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Car son âme, pendant sa vie, sera bénie: il vous louera, lorsque vous lui aurez fait du bien.
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
Il ira rejoindre les générations de ses pères, et durant l’éternité, il ne verra pas la lumière.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
L’homme, lorsqu’il était en honneur, ne l’a pas compris: il a été comparé aux animaux sans raison, et il est devenu semblable à eux.

< Zabura 49 >