< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
For the chief musician. A psalm of the sons of Korah. Hear this, all you peoples; give ear, all you inhabitants of the world,
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
both low and high, rich and poor together.
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
My mouth will speak wisdom and the meditation of my heart will be of understanding.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
I will incline my ear to a parable; I will begin my parable with the harp.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Why should I fear the days of evil, when iniquity surrounds me at my heels?
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
Why should I fear those who trust in their wealth and boast about the amount of their riches?
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
It is certain that no one can redeem his brother or give God a ransom for him,
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
For the redemption of one's life is costly, and no one can pay what we owe.
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
No one can live forever so that his body should not decay.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
For he will see decay. Wise men die; the fool and the brute alike perish and leave their wealth to others.
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
Their inner thought is that their families will continue forever, and the places where they live, to all generations; they call their lands after their own names.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
But man, having wealth, does not remain alive; he is like the beasts that perish.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
This, their way, is their folly; yet after them, men approve of their sayings. (Selah)
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
Like sheep they are appointed for Sheol, and death will be their shepherd. The upright will rule over them in the morning, and their bodies will be consumed in Sheol, with no place for them to live. (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
But God will redeem my life from the power of Sheol; he will receive me. (Selah) (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Do not be afraid when one becomes rich, and the glory of his house increases.
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
For when he dies he will take nothing away; his glory will not go down after him.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
He blessed his soul while he lived— and men praise you when you live for yourself—
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
he will go to the generation of his fathers and they will never see the light again.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
One who has wealth but no understanding is like the beasts, which perish.

< Zabura 49 >