< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
To the Chief Musician. For the Sons of Korah. A Melody. Hear ye, this all ye peoples, Give ear, all ye inhabitants of this passing world;
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
Both sons of the low, And sons of the high, —Together both rich and needy: —
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
My mouth, shall speak forth Wisdom, And the soft utterance of my heart be Understanding:
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
I will bend, to a by-word, mine ear, I will open, on the lyre, mine enigma.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Wherefore should I fear in the days of calamity, Though the iniquity of them who lie in wait for me should enclose me?
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
As for them who are trusting in their wealth, —And, in the abundance of their riches, do boast themselves,
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
A brother, can none of them, redeem, he cannot give unto God a ransom for himself:
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
So costly, is the redemption of their soul, That it faileth unto times age-abiding;
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
That he should, yet, live on, continually, Should not see corruption.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
For it is seen that, the wise, die, Together with the dullard, and the brutish, do they perish, And leave, to others, their wealth:
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
Their, inward thought, is that their houses are for times age-abiding, Their habitations, for generation after generation, —They give their own names unto lands!
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
But, a son of earth, though wealthy, cannot tarry, He hath made himself a by-word—Beasts, they resemble:
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
This, their way, is a folly to them, And yet, their followers, with their mouth, approve. (Selah)
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
Like sheep—into hades, are they driven, Death shall shepherd them, —And the upright shall have dominion over them in the morning, Even their form, is to decay, Hades, is all that remaineth of a habitation for him. (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
But, God, will redeem my soul, out of the hand of hades, For he will take me. (Selah) (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Do not fear, When a man becometh rich, When the glory of his house increaseth;
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
For, when he dieth, he shall take, nothing, his glory shall not descend after him;
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
For, though, his own self—while he lived, he used to bless, And they will praise thee, when thou doest well to thyself,
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
He shall enter as far as the circle of his fathers, Nevermore, shall they see the light.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
A son of earth though wealthy, who discerneth not, Hath made himself a by-word, Beasts, they resemble.

< Zabura 49 >