< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
For the Chief Musician; a Psalm of the sons of Korah. Hear this, all ye peoples; give ear, all ye inhabitants of the world:
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
Both low and high, rich and poor together.
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
My mouth shall speak wisdom; and the meditation of my heart shall be of understanding.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
I will incline mine ear to a parable: I will open my dark saying upon the harp.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Wherefore should I fear in the days of evil, when iniquity at my heels compasseth me about?
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
They that trust in their wealth, and boast themselves in the multitude of their riches;
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
None [of them] can by any means redeem his brother, nor give to God a ransom for him:
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
(For the redemption of their soul is costly, and must be let alone for ever: )
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
That he should still live alway, that he should not see corruption.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
For he seeth that wise men die, the fool and the brutish together perish, and leave their wealth to others.
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
Their inward thought is, [that] their houses [shall continue] for ever, [and] their dwelling places to all generations; they call their lands after their own names.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
But man abideth not in honour: he is like the beasts that perish.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
This their way is their folly: yet after them men approve their sayings. (Selah)
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
They are appointed as a flock for Sheol; death shall be their shepherd: and the upright shall have dominion over them in the morning; and their beauty shall be for Sheol to consume, that there be no habitation for it. (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
But God will redeem my soul from the power of Sheol: for he shall receive me. (Selah) (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Be not thou afraid when one is made rich, when the glory of his house is increased:
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
For when he dieth he shall carry nothing away; his glory shall not descend after him.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Though while he lived he blessed his soul, and men praise thee, when thou doest well to thyself,
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
He shall go to the generation of his fathers; they shall never see the light.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Man that is in honour, and understandeth not, is like the beasts that perish.

< Zabura 49 >