< Zabura 49 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
Přednímu kantoru z synů Chóre, žalm. Slyšte to všickni národové, pozorujte všickni obyvatelé zemští.
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
Tak z lidu obecného, jako z povýšených, tak bohatý, jako chudý.
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
Ústa má mluviti budou moudrost, a přemyšlování srdce mého rozumnost.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
Nakloním k přísloví ucha svého, a při harfě vykládati budu přípovídku svou.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
I proč se báti mám ve dnech zlých, aby nepravost těch, kteříž mi na paty šlapají, mne obklíčiti měla?
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
Kteříž doufají v svá zboží, a množstvím bohatství svého se chlubí.
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
Žádný bratra svého nijakž vykoupiti nemůže, ani Bohu za něj dáti mzdy vyplacení,
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
(Neboť by velmi drahé musilo býti vyplacení duše jejich, protož nedovedeť toho na věky),
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
Aby živ byl věčně, a neviděl porušení.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
Nebo se vídá, že i moudří umírají, blázen a hovadný člověk zaroveň hynou, zboží svého i cizím zanechávajíce.
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
Myšlení jejich jest, že domové jejich věční jsou, a příbytkové jejich od národu do pronárodu; pročež je po krajinách nazývají jmény svými.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Ale člověk v slávě netrvá, jsa podobný hovadům, kteráž hynou.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
Taková snažnost jejich jest bláznovstvím při nich, však potomci jejich ústy svými to schvalují. (Sélah)
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol )
Jako hovada v pekle skladeni budou, smrt je žráti bude, ale upřímí panovati budou nad nimi v jitře; způsob pak oněchno aby zvetšel, z příbytku svého octnou se v hrobě. (Sheol )
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol )
Ale Bůh vykoupí duši mou z moci pekla, když mne přijme. (Sélah) (Sheol )
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Neboj se, když by někdo zbohatl, a když by se rozmnožila sláva domu jeho.
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
Při smrti zajisté ničeho nevezme, aniž sstoupí za ním sláva jeho.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Ačťkoli duši své, pokudž jest živ, lahodí; k tomu chválí jej i jiní, když sobě čistě povoluje:
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
A však musí se odebrati za věkem otců svých, a na věky světla neuzří.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Summou: Člověk jsa ve cti, neusrozumí-li sobě, bývá učiněn podobný hovadům, kteráž hynou.