< Zabura 48 >

1 Waƙa ce. Zabura ta’ya’yan Kora maza. Ubangiji mai girma ne, kuma mafificin yabo, a birnin Allahnmu, dutsensa mai tsarki.
[Ein Lied, ein Psalm. [Eig. Ein Psalm-Lied] Von den Söhnen Korahs.] Groß ist Jehova und sehr zu loben in der Stadt unseres Gottes auf seinem heiligen Berge.
2 Kyakkyawa ce cikin tsayinta, abin farin cikin dukan duniya. Kamar ƙwanƙoli mafi tsayi na Zafon ne Dutsen Sihiyona, birnin Babban Sarki.
Schön ragt empor, eine Freude der ganzen Erde, der Berg Zion, an der Nordseite, die Stadt des großen Königs.
3 Allah yana cikin fadodinta; ya nuna kansa mafaka ce gare ta.
Gott ist bekannt in ihren Palästen als eine hohe Feste.
4 Sa’ad da sarakuna suka haɗa rundunoni, sa’ad da suka yi gaba tare,
Denn siehe, die Könige hatten sich versammelt, waren herangezogen allesamt.
5 sun gan ta suka kuwa yi mamaki; suka gudu don tsoro.
Sie sahen, da erstaunten sie; sie wurden bestürzt, flohen ängstlich hinweg.
6 Rawar jiki ya kama su a can, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Beben ergriff sie daselbst, Angst, der Gebärenden gleich.
7 Ka hallaka su kamar jiragen ruwan Tarshish da iskar gabas ta wargaje.
Durch den Ostwind zertrümmertest du die Tarsisschiffe.
8 Yadda muka ji, haka muka gani a cikin birnin Ubangiji Maɗaukaki, a cikin birnin Allahnmu. Allah ya sa ta zauna lafiya har abada. (Sela)
Wie wir gehört hatten, also haben wir es gesehen in der Stadt Jehovas der Heerscharen, in der Stadt unseres Gottes: Gott wird sie befestigen bis in Ewigkeit. (Sela)
9 Cikin haikalinka, ya Allah, mun yi tunani a kan ƙaunarka marar ƙarewa.
Wir haben gedacht, o Gott, an deine Güte, im Innern deines Tempels.
10 Kamar sunanka, ya Allah, yabonka ya kai iyakokin duniya; hannunka na dama ya cika da adalci.
Wie dein Name, Gott, also ist dein Lob [O. Ruhm] bis an die Enden der Erde; mit Gerechtigkeit ist gefüllt deine Rechte.
11 Dutsen Sihiyona ya yi farin ciki, ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukuntanka.
Es freue sich der Berg Zion, es mögen frohlocken die Töchter Judas um deiner Gerichte willen!
12 Yi tafiya cikin Sihiyona, ku kewaye ta, ku ƙirga hasumiyoyinta,
Umgehet Zion und umkreiset es, zählet seine Türme;
13 ku lura da katangarta da kyau, ku dubi fadodinta, don ku faɗe su ga tsara mai zuwa.
Betrachtet genau seine Wälle, mustert [O. durchschreitet] seine Paläste, damit ihrs erzählet dem künftigen Geschlecht!
14 Gama wannan Allah shi ne Allahnmu har abada abadin; zai zama jagorarmu har zuwa ƙarshe.
Denn dieser Gott ist unser Gott immer und ewiglich! Er wird uns leiten bis an den Tod.

< Zabura 48 >