< Zabura 48 >

1 Waƙa ce. Zabura ta’ya’yan Kora maza. Ubangiji mai girma ne, kuma mafificin yabo, a birnin Allahnmu, dutsensa mai tsarki.
“A psalm of the sons of Korah.” Great is Jehovah, and greatly to be praised In the city of our God, upon his holy mountain.
2 Kyakkyawa ce cikin tsayinta, abin farin cikin dukan duniya. Kamar ƙwanƙoli mafi tsayi na Zafon ne Dutsen Sihiyona, birnin Babban Sarki.
Beautiful in its elevation is Mount Zion, The joy of the whole earth; The joy of the farthest North is the city of the great king;
3 Allah yana cikin fadodinta; ya nuna kansa mafaka ce gare ta.
In her palaces God is known as a refuge.
4 Sa’ad da sarakuna suka haɗa rundunoni, sa’ad da suka yi gaba tare,
For, lo! kings were assembled against it; They passed away together.
5 sun gan ta suka kuwa yi mamaki; suka gudu don tsoro.
As soon as they saw, they were astonished; They were confounded, and hasted away.
6 Rawar jiki ya kama su a can, zafi kamar na mace mai naƙuda.
There terror seized upon them, —Pain, as of a woman in travail;
7 Ka hallaka su kamar jiragen ruwan Tarshish da iskar gabas ta wargaje.
As when the east wind breaketh in pieces The ships of Tarshish.
8 Yadda muka ji, haka muka gani a cikin birnin Ubangiji Maɗaukaki, a cikin birnin Allahnmu. Allah ya sa ta zauna lafiya har abada. (Sela)
As we have heard, so have we seen In the city of the LORD of hosts, in the city of our God; God will establish it for ever. (Pause)
9 Cikin haikalinka, ya Allah, mun yi tunani a kan ƙaunarka marar ƙarewa.
We think of thy loving-kindness, O God! In the midst of thy temple!
10 Kamar sunanka, ya Allah, yabonka ya kai iyakokin duniya; hannunka na dama ya cika da adalci.
As thy name, O God! so thy praise, extendeth to the ends of the earth; Thy right hand is full of righteousness.
11 Dutsen Sihiyona ya yi farin ciki, ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukuntanka.
Mount Zion rejoiceth, The daughters of Judah exult, On account of thy righteous judgments.
12 Yi tafiya cikin Sihiyona, ku kewaye ta, ku ƙirga hasumiyoyinta,
Go round about Zion; number her towers;
13 ku lura da katangarta da kyau, ku dubi fadodinta, don ku faɗe su ga tsara mai zuwa.
Mark well her bulwarks; count her palaces; That ye may tell it to the next generation!
14 Gama wannan Allah shi ne Allahnmu har abada abadin; zai zama jagorarmu har zuwa ƙarshe.
For this God is our God for ever and ever; He will be our guide unto death.

< Zabura 48 >