< Zabura 48 >
1 Waƙa ce. Zabura ta’ya’yan Kora maza. Ubangiji mai girma ne, kuma mafificin yabo, a birnin Allahnmu, dutsensa mai tsarki.
A Song; a Psalm. Of the sons of Korah. Great is Jehovah, and greatly to be praised in the city of our God, in the hill of his holiness.
2 Kyakkyawa ce cikin tsayinta, abin farin cikin dukan duniya. Kamar ƙwanƙoli mafi tsayi na Zafon ne Dutsen Sihiyona, birnin Babban Sarki.
Beautiful in elevation, the joy of the whole earth, is mount Zion, [on] the sides of the north, the city of the great King.
3 Allah yana cikin fadodinta; ya nuna kansa mafaka ce gare ta.
God is known in her palaces as a high fortress.
4 Sa’ad da sarakuna suka haɗa rundunoni, sa’ad da suka yi gaba tare,
For behold, the kings assembled themselves, they passed by together;
5 sun gan ta suka kuwa yi mamaki; suka gudu don tsoro.
They saw, — so they marvelled; they were troubled, they fled in consternation:
6 Rawar jiki ya kama su a can, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Trembling took hold upon them there; anguish, as of a woman in travail.
7 Ka hallaka su kamar jiragen ruwan Tarshish da iskar gabas ta wargaje.
With an east wind thou hast broken the ships of Tarshish.
8 Yadda muka ji, haka muka gani a cikin birnin Ubangiji Maɗaukaki, a cikin birnin Allahnmu. Allah ya sa ta zauna lafiya har abada. (Sela)
As we have heard, so have we seen, in the city of Jehovah of hosts, in the city of our God: God doth establish it for ever. (Selah)
9 Cikin haikalinka, ya Allah, mun yi tunani a kan ƙaunarka marar ƙarewa.
We have thought, O God, of thy loving-kindness, in the midst of thy temple.
10 Kamar sunanka, ya Allah, yabonka ya kai iyakokin duniya; hannunka na dama ya cika da adalci.
According to thy name, O God, so is thy praise unto the ends of the earth: thy right hand is full of righteousness.
11 Dutsen Sihiyona ya yi farin ciki, ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukuntanka.
Let mount Zion rejoice, let the daughters of Judah be glad, because of thy judgments.
12 Yi tafiya cikin Sihiyona, ku kewaye ta, ku ƙirga hasumiyoyinta,
Walk about Zion, and go round about her: count the towers thereof;
13 ku lura da katangarta da kyau, ku dubi fadodinta, don ku faɗe su ga tsara mai zuwa.
Mark ye well her bulwarks, consider her palaces: that ye may tell it to the generation following.
14 Gama wannan Allah shi ne Allahnmu har abada abadin; zai zama jagorarmu har zuwa ƙarshe.
For this God is our God for ever and ever; he will be our guide until death.