< Zabura 47 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
För sångmästaren; av Koras söner; en psalm. Klappen i händerna, alla folk, höjen jubel till Gud med fröjderop.
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
Ty HERREN är den Högste, fruktansvärd är han, en stor konung över hela jorden.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
Han tvingar folk under oss och folkslag under våra fötter.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
Han utväljer åt oss vår arvedel, Jakobs, hans älskades, stolthet. (Sela)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
Gud har farit upp under jubel, HERREN, under basuners ljud.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Lovsjungen Gud, lovsjungen; lovsjungen vår konung, lovsjungen.
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
Ty Gud är konung över hela jorden; lovsjungen honom med en sång.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
Gud är nu konung över hedningarna, Gud har satt sig på sin heliga tron.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Folkens ypperste hava församlat sig till att bliva ett Abrahams Guds folk. Ty Gud tillhöra de som äro jordens sköldar; högt är han upphöjd.