< Zabura 47 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
För sångmästaren; av Koras söner; en psalm.
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
Klappen i händerna, alla folk, höjen jubel till Gud med fröjderop.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
Ty HERREN är den Högste, fruktansvärd är han, en stor konung över hela jorden.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
Han tvingar folk under oss och folkslag under våra fötter.
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
Han utväljer åt oss vår arvedel, Jakobs, hans älskades, stolthet. (Sela)
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Gud har farit upp under jubel, HERREN, under basuners ljud.
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
Lovsjungen Gud, lovsjungen; lovsjungen vår konung, lovsjungen.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
Ty Gud är konung över hela jorden; lovsjungen honom med en sång.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Gud är nu konung över hedningarna, Gud har satt sig på sin heliga tron. Folkens ypperste hava församlat sig till att bliva ett Abrahams Guds folk. Ty Gud tillhöra de som äro jordens sköldar; högt är han upphöjd.