< Zabura 47 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
Todos los pueblos batid las manos: clamád a Dios con voz de alegría.
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
Porque Jehová es sublime y temeroso: Rey grande sobre toda la tierra.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
Él someterá a los pueblos debajo de nosotros, y a las naciones debajo de nuestros pies.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
El nos eligirá nuestras heredades; la hermosura de Jacob, al cual amó. (Selah)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
Subió Dios con júbilo, Jehová con voz de trompeta.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Cantád a Dios, cantád; cantád a nuestro Rey, cantád.
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
Porque el Rey de toda la tierra es Dios: cantád entendiendo.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
Reinó Dios sobre las naciones: Dios se asentó sobre su santo trono.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Los príncipes de los pueblos se juntaron al pueblo del Dios de Abraham: porque de Dios son los escudos de la tierra; él es muy ensalzado.

< Zabura 47 >