< Zabura 47 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
KOMAIL kainok karos lopolop o kapinga Kot ki ngil kaperen!
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
Pwe Ieowa me lapalap kaualap, a meid kalank; i Nanmarki lapalap nin sap akan karos.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
A kotin kaloedi ong kitail wei kan o aramas akan pan nä atail.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
A kotin piladang kitail atail soso, lingan en Iakop, me a kotin pok ong. (Sela)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
Kot kotida ngisingis, o Ieowa ki ngil en koronete kelail.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Kauli ong Kot psalm ko! Kaulki psalm ko! Kauli ong atail Nanmarki! Kakaul!
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
Pwe Kot Nanmarki nan sap karos; komail kaul ki psalm ni lolekong.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
Kot Nanmarki en men liki kan; Kot kotikot pon mol a saraui.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Saupeidi en wei kan pokon pena wiala wein Kot en Apraam; pwe pere en mauin nin sappa me sapwilim en Kot. A kotin lapalap melel.