< Zabura 47 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
In finem, pro filiis Core. Psalmus. [Omnes gentes, plaudite manibus; jubilate Deo in voce exsultationis:
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
quoniam Dominus excelsus, terribilis, rex magnus super omnem terram.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
Subjecit populos nobis, et gentes sub pedibus nostris.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
Elegit nobis hæreditatem suam; speciem Jacob quam dilexit.
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
Ascendit Deus in jubilo, et Dominus in voce tubæ.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Psallite Deo nostro, psallite; psallite regi nostro, psallite:
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
quoniam rex omnis terræ Deus, psallite sapienter.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
Regnabit Deus super gentes; Deus sedet super sedem sanctam suam.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Principes populorum congregati sunt cum Deo Abraham, quoniam dii fortes terræ vehementer elevati sunt.]

< Zabura 47 >