< Zabura 47 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
聖歌隊の指揮者によってうたわせたコラの子の歌 もろもろの民よ、手をうち、喜びの声をあげ、神にむかって叫べ。
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
いと高き主は恐るべく、全地をしろしめす大いなる王だからである。
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
主はもろもろの民をわれらに従わせ、もろもろの国をわれらの足の下に従わせられた。
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
主はその愛されたヤコブの誇をわれらの嗣業として、われらのために選ばれた。 (セラ)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
神は喜び叫ぶ声と共にのぼり、主はラッパの声と共にのぼられた。
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
神をほめうたえよ、ほめうたえよ、われらの王をほめうたえよ、ほめうたえよ。
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
神は全地の王である。巧みな歌をもってほめうたえよ。
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
神はもろもろの国民を統べ治められる。神はその聖なるみくらに座せられる。
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
もろもろの民の君たちはつどい来て、アブラハムの神の民となる。地のもろもろの盾は神のものである。神は大いにあがめられる。

< Zabura 47 >