< Zabura 47 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
Dem Sangmeister für die Söhne Korachs. Ein Psalm. Ihr Völker alle, klatschet in die Hände, jubelt zu Gott mit der Stimme der Lobpreisung.
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
Denn Jehovah, der Allerhöchste, ist furchtbar, ein großer König über alle Erde.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
Er bezwingt Völker unter uns, und Volksstämme unter unsere Füße.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
Er hat uns unser Erbe auserwählt, Jakobs Stolz, den Er geliebt. (Selah)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
Hinauf steigt Gott mit Jubel, Jehovah mit der Stimme der Posaune.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Singt Psalmen unserem Gott, singt Psalmen; singt Psalmen unserem König, singt Psalmen!
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
Denn König der ganzen Erde ist Gott, singt Ihm Psalmen verständig.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
Gott ist König über Völkerschaften, Gott sitzt auf dem Thron Seiner Heiligkeit.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Der Völker Freiwillige haben sich versammelt, das Volk des Gottes Abrahams; denn Gottes sind der Erde Schilder; sehr erhöht ist Er.